< Irmiya 2 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
2 “Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
Va, et crie, ceux de Jérusalem l'entendant, et dis: Ainsi a dit l'Eternel: il me souvient [pour l'amour] de toi de la compassion que j'ai eue pour toi en ta jeunesse, et de l'amour de tes épousailles, quand tu venais après moi dans le désert, en un pays qu'on ne sème point.
3 Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
Israël était une chose sainte à l'Eternel, c'étaient les prémices de son revenu; tous ceux qui le dévoraient étaient [trouvés] coupables, il leur en arrivait du mal, dit l'Eternel.
4 Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
Ecoutez la parole de l'Eternel, maison de Jacob, et vous toutes les familles de la maison d'Israël:
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
Ainsi a dit l'Eternel: quelle injustice ont trouvée vos pères en moi, qu'ils se soient éloignés de moi, qu'ils aient marché après la vanité, et qu'ils soient devenus vains?
6 Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
Et ils n'ont point dit: où est l'Eternel qui nous a fait remonter du pays d'Egypte, qui nous a conduits par un désert, par un pays de landes et montagneux, par un pays aride et d'ombre de mort, par un pays où aucun homme n'avait passé, et où personne n'avait habité?
7 Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
Car je vous ai fait entrer dans un pays de Carmel, afin que vous mangeassiez ses fruits, et de ses biens; mais sitôt que vous [y] êtes entrés, vous avez souillé mon pays, et avez rendu abominable mon héritage.
8 Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
Les Sacrificateurs n'ont point dit: où est l'Eternel? Et ceux qui expliquaient la Loi, ne m'ont point connu; et les pasteurs ont prévariqué contre moi, et les prophètes ont prophétisé de par Bahal, et ont marché après des choses qui ne profitent de rien.
9 “Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
Pour cette cause encore je plaiderai avec vous, dit l'Eternel, et je plaiderai avec les enfants de vos enfants.
10 Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
Car passez par les Îles de Kittim, et voyez; envoyez en Kédar, et considérez bien, et regardez s'il y a eu rien de tel.
11 Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
Y a-t-il aucune nation qui ait changé de dieux, lesquels toutefois ne [sont] pas dieux? Mais mon peuple a changé sa gloire en ce qui ne profite de rien.
12 Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
Cieux soyez étonnés de ceci; ayez-[en] de l'horreur, et soyez extrêmement asséchés, dit l'Eternel.
13 “Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
Car mon peuple a fait deux maux; ils m'ont abandonné, moi [qui suis] la source des eaux vives, pour se creuser des citernes, des citernes crevassées qui ne peuvent point contenir d'eau.
14 Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
Israël est-il un esclave, ou un esclave né dans la maison? pourquoi donc a-t-il été mis au pillage?
15 Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
Les lionceaux ont rugi, et ont jeté leur cri sur lui; et on a mis leur pays en désolation, ses villes ont été brûlées, de sorte qu'il n'y a personne qui y habite.
16 Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
Même les enfants de Noph, et de Taphnés te casseront le sommet de la tête.
17 Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
Ne t'es-tu pas fait cela parce que tu as abandonné l'Eternel ton Dieu, dans le temps qu'il te menait par le chemin?
18 To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
Et maintenant, qu'as-tu affaire d'aller en Egypte pour y boire de l'eau de Sihor? et qu'as-tu affaire d'aller en Assyrie, pour y boire de l'eau du fleuve?
19 Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ta malice te châtiera, et tes débauches te réprimanderont, afin que tu saches et que tu voies que c'est une chose mauvaise et amère, que tu aies abandonné l'Eternel ton Dieu, et que tu ne sois point rempli de ma frayeur, dit le Seigneur l'Eternel des armées.
20 “Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
Parce que depuis longtemps j'ai brisé ton joug, et rompu tes liens, tu as dit: je ne serai plus dans la servitude; c'est pourquoi tu as erré en te prostituant sur toute haute colline, et sous tout arbre vert.
21 Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
Or je t'avais moi-même plantée [comme] une vigne exquise, de laquelle tout le plant était franc; comment donc t'es-tu changée en sarments d'une vigne abâtardie?
22 Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Quand tu te laverais avec du nitre, et que tu prendrais beaucoup de savon, ton iniquité [demeurerait] encore marquée devant moi, dit le Seigneur l'Eternel.
23 “Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
Comment dis-tu: je ne me suis point souillée, je ne suis point allée après les Bahalins? Regarde ton train dans la vallée, reconnais ce que tu as fait, dromadaire légère, qui ne tiens point de route certaine.
24 kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
Anesse sauvage, accoutumée au désert, humant le vent à son plaisir; et qui est-ce qui lui pourrait faire rebrousser sa course? nul de ceux qui la cherchent ne se lassera après elle, on la trouvera en son mois.
25 Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
Retiens ton pied, que tu ne marches déchaussée, et ton gosier, que tu ne sois altérée. Mais tu as dit: c'en est fait. Non; car j'aime les étrangers, et j'irai après eux.
26 “Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
Comme le larron est confus, quand il est surpris, ainsi sont confus ceux de la maison d'Israël, eux, leurs Rois, les principaux d'entre eux, leurs Sacrificateurs, et leurs Prophètes;
27 Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
Qui disent au bois: tu es mon père; et à la pierre: tu m'as engendré. Car ils m'ont tourné le dos, et non pas la face; puis ils disent dans le temps de leur calamité: lève-toi, et nous délivre.
28 To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
Et où sont tes dieux que tu t'es faits? qu'ils se lèvent pour voir s'ils te délivreront au temps de la calamité; car, ô Juda! tu as eu autant de dieux que de villes.
29 “Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
Pourquoi plaideriez-vous contre moi? vous avez tous péché contre moi, dit l'Eternel.
30 “A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
J'ai frappé en vain vos enfants, ils n'ont point reçu d'instruction; votre épée a dévoré vos Prophètes, comme un lion qui ravage [tout].
31 “Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
Ô race! considérez vous-mêmes la parole de l'Eternel, [qui dit]: Ai-je été un désert à Israël? ai-je été une terre toute ténébreuse? Pourquoi mon peuple a-t-il dit: nous sommes les maîtres; nous ne viendrons plus à toi?
32 Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
La vierge oubliera-t-elle son ornement? l'épouse ses atours? mais mon peuple m'a oublié durant des jours sans nombre.
33 Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
Pourquoi rends-tu ainsi affectée ta contenance pour chercher des amoureux, en sorte que tu as même enseigné tes manières de faire aux femmes de mauvaise vie?
34 A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
Même dans les pans de ta robe a été trouvé le sang des âmes des pauvres innocents, que tu n'avais point surpris en fracture, mais il y a été trouvé pour toutes ces choses-là.
35 kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
Et tu dis: je suis innocente; quoi qu'il en soit, sa colère s'est détournée de moi. Voici, je m'en vais contester contre toi, sur ce que tu as dit: je n'ai point péché.
36 Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
Pourquoi te donnes-tu tant de mouvement, changeant de chemin? tu seras aussi confuse d'Egypte, que tu as été confuse d'Assyrie.
37 Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.
Tu sortiras même d'ici, ayant tes mains sur ta tête, parce que l'Eternel a rejeté les fondements de ta confiance, et tu n'auras aucune prospérité par eux.

< Irmiya 2 >