< Irmiya 2 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
2 “Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
“Go, and you have called in the ears of Jerusalem, saying, Thus said YHWH: I have remembered for you The kindness of your youth, the love of your espousals, Your going after Me in a wilderness, in a land not sown.
3 Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
Israel [is] holy to YHWH, The first-fruit of His increase, All consuming him are guilty, Calamity comes to them,” A declaration of YHWH.
4 Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
Hear a word of YHWH, O house of Jacob, And all you families of the house of Israel—
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
Thus said YHWH: “What perversity have your fathers found in Me, That they have gone far off from Me, And go after vanity, and become vain,
6 Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
And have not said, Where [is] YHWH, Who brings us up out of the land of Egypt, Who leads us in a wilderness, In a land of deserts and pits, In a dry land, and of death-shade, In a land that none has passed through, Nor has man dwelt there?
7 Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
Indeed, I bring you into a land of fruitful fields, To eat its fruit and its goodness, And you come in and defile My land, And have made My inheritance an abomination.
8 Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
The priests have not said, Where [is] YHWH? And those handling the Law have not known Me. And the shepherds transgressed against Me, And the prophets have prophesied by Ba‘al, And have gone after those who do not profit.
9 “Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
Therefore, I yet plead with you,” A declaration of YHWH, “And I plead with your sons’ sons.
10 Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
For pass to the islands of Chittim and see, And send to Kedar and consider well, And see if there has been [anything] like this:
11 Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
Has a nation changed gods? (And they [are] no gods!) And My people has changed its glory For that which does not profit.
12 Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
Be astonished, you heavens, at this, Indeed, be frightened, be greatly desolated,” A declaration of YHWH.
13 “Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
“For My people have done two evils, They have forsaken Me, a fountain of living waters, To hew out for themselves wells—broken wells, That do not contain the waters.
14 Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
[Is] Israel a servant? Is he a child of the house? Why has he been for a prey?
15 Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
Young lions roar against him, They have given forth their voice, And make his land become a desolation, His cities have been burned without inhabitant.
16 Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
Also sons of Noph and Tahapanes Consume you—the crown of the head!
17 Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
Do you not do this to yourself? [By] your forsaking your God YHWH, At the time He is leading you in the way?
18 To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
And now, why do you [go] in the way of Egypt, To drink the waters of Sihor? And why do you [go] in the way of Asshur, To drink the waters of the River?
19 Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Your wickedness instructs you, And your backslidings reprove you, Know and see that an evil and a bitter thing [is] your forsaking your God YHWH, And My fear not being on you,” A declaration of Lord YHWH of Hosts.
20 “Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
“For from of old you have broken your yoke, Drawn away your bands, and say, I do not serve, For on every high height, and under every green tree, You are wandering—a harlot.
21 Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
And I planted you [as] a choice vine, wholly of true seed, And how have you been turned Into the degenerate shoots of a strange vine to Me?
22 Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
But though you wash with natron, And multiply soap to yourself, Your iniquity is marked before Me,” A declaration of Lord YHWH.
23 “Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
“How can you say, I have not been defiled, I have not gone after the Ba‘alim? See your way in a valley, know what you have done, A swift dromedary winding her ways,
24 kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
A wild donkey accustomed to a wilderness, She has swallowed up wind in the desire of her soul, Her meeting—who turns her back? None seeking her weary themselves, In her month they find her.
25 Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
Withhold your foot from being unshod, And your throat from thirst, And you say, It is incurable, No, for I have loved strangers, and I go after them.
26 “Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
As the shame of a thief when he is found, So has the house of Israel been put to shame, They, their kings, their heads, And their priests, and their prophets,
27 Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
Saying to wood, You [are] my father! And to a stone, You have brought me forth, For they turned to me the back and not the face, And in the time of their distress, They say, Arise, and save us.
28 To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
And where [are] your gods, that you have made to yourself? Let them arise, if they may save you, In the time of your distress, For—the number of your cities have been your gods, O Judah,
29 “Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
Why do you strive with Me? All of you have transgressed against Me,” A declaration of YHWH.
30 “A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
“I have struck your sons in vain, They have not accepted instruction, Your sword has devoured your prophets, As a destroying lion.
31 “Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
O generation, see the word of YHWH: Have I been a wilderness to Israel? A land of thick darkness? Why have My people said, We wandered freely, We do not come to You again.
32 Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
Does a virgin forget her ornaments? A bride her bands? And My people have forgotten Me [for] days without number.
33 Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
Why do you make your ways pleasing to seek love? Therefore you have even taught the wicked your ways.
34 A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
Also the blood of innocent needy souls Has been found on your skirts, I have not found them by digging, But on all these.
35 kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
And you say, Because I have been innocent, Surely His anger has turned back from me? Behold, I have been judged with you, Because of your saying, I have not sinned.
36 Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
What? You are very vile to repeat your way, You are even ashamed of Egypt, As you have been ashamed of Asshur,
37 Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.
Also you go out from this, And your hands on your head, For YHWH has kicked at your confidences, And you do not give prosperity to them!”

< Irmiya 2 >