< Irmiya 19 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Assim disse Javé: “Vá e compre um recipiente de barro de oleiro, e leve alguns dos anciãos do povo e dos anciãos dos sacerdotes;
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
e saia para o vale do filho de Hinnom, que é pela entrada do portão Harsith, e proclame lá as palavras que eu lhe direi.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Diga: 'Ouçam a palavra de Javé, reis de Judá e habitantes de Jerusalém': Javé dos Exércitos, o Deus de Israel diz: “Eis que eu trarei o mal sobre este lugar, o qual, quem ouvir, seus ouvidos formigarão.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
Porque me abandonaram, e contaminaram este lugar, e queimaram incenso nele para outros deuses que não conheciam - eles, seus pais e os reis de Judá - e encheram este lugar com o sangue de inocentes,
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
e construíram os lugares altos de Baal para queimar seus filhos no fogo para holocaustos a Baal, que eu não comandei, nem falei, que nem sequer entrou em minha mente.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
Portanto, eis que vêm os dias”, diz Javé, “que este lugar não será mais chamado 'Topheth', nem 'The Valley of the son of Hinnom', mas 'The valley of Slaughter'.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
““““Vou invalidar o conselho de Judá e Jerusalém neste lugar. Farei com que caiam pela espada diante de seus inimigos, e pela mão daqueles que buscam sua vida”. Darei seus corpos mortos para serem alimento para as aves do céu e para os animais da terra”.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
Vou fazer desta cidade um espanto e um assobio. Todos os que passarem por ela ficarão espantados e assobiarão por causa de todas as suas pragas.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
Eu os farei comer a carne de seus filhos e a carne de suas filhas. Cada um deles comerá a carne de seu amigo no cerco e na angústia com que seus inimigos, e aqueles que procuram sua vida, os afligirão”.
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
“Então você quebrará o recipiente à vista dos homens que vão com você,
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
e lhes dirá: 'Yahweh dos Exércitos diz: “Mesmo assim quebrarei este povo e esta cidade quando alguém quebrar um vaso de oleiro, que não pode ficar inteiro novamente. Eles vão enterrar em Topheth até que não haja lugar para enterrar.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
Isto é o que farei com este lugar”, diz Yahweh, “e com seus habitantes, até mesmo fazendo desta cidade como Topheth”.
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
As casas de Jerusalém e as casas dos reis de Judá, que estão contaminadas, serão como o lugar de Topheth, mesmo todas as casas em cujos telhados queimaram incenso para todo o exército do céu e derramaram ofertas de bebida para outros deuses”””.
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Então Jeremias veio de Topheth, onde Iavé o havia enviado para profetizar, e ficou na corte da casa de Iavé, e disse a todo o povo:
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
“Iavé dos Exércitos, o Deus de Israel diz: 'Eis que trarei sobre esta cidade e sobre todas as suas cidades todo o mal que pronunciei contra ela, porque endureceram o pescoço, para que não ouçam minhas palavras'”.

< Irmiya 19 >