< Irmiya 19 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Ainsi parle Yahvé: Va, achète un vase de terre de potier, prends quelques anciens du peuple et des anciens des prêtres,
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
et va dans la vallée du fils de Hinnom, qui est à l'entrée de la porte Harsith, et proclame là les paroles que je te dirai.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Dites: « Écoutez la parole de Yahvé, rois de Juda et habitants de Jérusalem: Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici que je vais faire venir sur ce lieu un malheur dont l'oreille de celui qui l'entendra frissonnera.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
Parce qu'ils m'ont abandonné, parce qu'ils ont souillé ce lieu, parce qu'ils y ont offert de l'encens à d'autres dieux qu'ils ne connaissaient pas, eux, leurs pères, et les rois de Juda, parce qu'ils ont rempli ce lieu du sang des innocents,
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
parce qu'ils ont bâti les hauts lieux de Baal, et qu'ils ont brûlé leurs enfants au feu en holocauste à Baal, ce que je n'ai ni ordonné, ni dit, ce qui ne m'est pas venu à l'esprit.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
C'est pourquoi voici, les jours viennent, dit Yahvé, où ce lieu ne sera plus appelé Topheth, ni vallée du fils de Hinnom, mais vallée du carnage.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
"''Je réduirai à néant le conseil de Juda et de Jérusalem en ce lieu. Je les ferai tomber par l'épée devant leurs ennemis, et par la main de ceux qui en veulent à leur vie. Je donnerai leurs cadavres en pâture aux oiseaux du ciel et aux animaux de la terre.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
Je ferai de cette ville un objet d'étonnement et un sifflement. Tous ceux qui passeront près d'elle seront étonnés et siffleront à cause de tous ses fléaux.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
Je leur ferai manger la chair de leurs fils et la chair de leurs filles. Ils mangeront chacun la chair de leur ami dans le siège et dans la détresse avec lesquels leurs ennemis, et ceux qui en veulent à leur vie, les accableront. »''
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
« Puis tu briseras le récipient sous les yeux des hommes qui t'accompagnent,
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
et tu leur diras: « Yahvé des armées dit: « Je briserai ce peuple et cette ville comme on brise le vase d'un potier, qui ne peut plus être reconstitué. Ils enterreront à Topheth jusqu'à ce qu'il n'y ait plus de place pour enterrer.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
C'est ce que je ferai à ce lieu, dit Yahvé, et à ses habitants, et je rendrai cette ville semblable à Topheth.
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
Les maisons de Jérusalem et les maisons des rois de Juda, qui sont souillées, seront comme le lieu de Topheth, toutes les maisons sur les toits desquelles on a brûlé de l'encens à toute l'armée du ciel et versé des libations à d'autres dieux. »'"
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Jérémie revint de Topheth, où Yahvé l'avait envoyé prophétiser, et il se tint dans le parvis de la maison de Yahvé, et dit à tout le peuple:
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
« Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici, je vais faire venir sur cette ville et sur toutes ses cités tous les malheurs que j'ai prononcés contre elle, parce qu'ils ont raidi leur cou pour ne pas entendre mes paroles. »

< Irmiya 19 >