< Irmiya 19 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Yahweh said this, “Go and purchase a potter's clay flask while you are with the elders of the people and the priests.
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
Then go out to the Valley of Ben Hinnom at the entry of the Broken Pottery Gate, and there proclaim the words that I will tell you.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Say, 'Hear the word of Yahweh, kings of Judah and inhabitants of Jerusalem! Yahweh of hosts, God of Israel, says this, “See, I am about to bring disaster on this place, and the ears of everyone who hears of it will tingle.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
I will do this because they have abandoned me and profaned this place. In this place they offer sacrifices to other gods that they did not know. They, their ancestors, and the kings of Judah have also filled this place with innocent blood.
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
They built the high places of Baal to burn their sons in the fire as burnt offerings to him—something that I did not command or mention, nor did it enter my mind.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
Therefore, see, the days are coming—this is Yahweh's declaration—when this place will no longer be called Topheth, the Valley of Ben Hinnom, for it will be the Valley of Slaughter.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
In this place I will make the plans of Judah and Jerusalem useless. I will make them to fall by the sword before their enemies and by the hand of the ones seeking their lives. Then I will give their corpses as food to the birds of the heavens and the beasts of the earth.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
Then I will make this city a ruin and the object of hissing, for everyone passing by it will shudder and hiss regarding all of its plagues.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
I will make them eat the flesh of their sons and daughters; each man will consume the flesh of his neighbor in the siege and in the anguish brought on them by their enemies and the ones seeking their lives.”'
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
Then you will break the clay flask in the sight of the men who went with you.
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
You will say to them, 'Yahweh of hosts says this: I will do this same thing to this people and this city—this is Yahweh's declaration—just as Jeremiah shattered the clay flask so that it could not be repaired again. People will bury the dead in Topheth until there is no place left for any more dead.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
This is what I will do to this place and its inhabitants when I make this city like Topheth—this is Yahweh's declaration—
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
so the houses of Jerusalem and of the kings of Judah will become like Topheth—all the houses on whose rooftops the unclean people worship all the stars of the heavens and pour out drink offerings to other gods.'”
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Then Jeremiah went from Topheth, where Yahweh had sent him to prophesy. He stood in the courtyard of Yahweh's house and he said to all the people,
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
“Yahweh of hosts, God of Israel, says this, 'See, I am about to bring to this city and to all of its towns all the disaster that I have proclaimed against it, since they stiffened their neck and refused to listen to my words.'”

< Irmiya 19 >