< Irmiya 19 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Thus he said Yahweh go and you will buy a bottle of a potter of earthenware and some of [the] elders of the people and some of [the] elders of the priests.
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
And you will go out to [the] valley of Ben Hinnom which [is at] [the] entrance of [the] gate of (the potsherd *Q(k)*) and you will proclaim there the words which I will speak to you.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
And you will say hear [the] word of Yahweh O kings of Judah and [the] inhabitants of Jerusalem thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel here I [am] about to bring calamity on the place this which every [one who] hears of it they will tingle ears his.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
Because - that they have forsaken me and they have treated as foreign the place this and they have made smoke in it to gods other which not they knew them they and ancestors their and [the] kings of Judah and they have filled the place this [the] blood of innocent [ones].
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
And they have built [the] high places of Baal to burn children their in the fire burnt offerings to Baal which not I commanded and not I spoke and not it came up on heart my.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
Therefore here! days [are] coming [the] utterance of Yahweh and not it will be called to the place this again Topheth and [the] valley of Ben Hinnom that except [the] valley of slaughter.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
And I will make void [the] plan of Judah and Jerusalem in the place this and I will make fall them by the sword before enemies their and by [the] hand of [those who] seek life their and I will give corpse[s] their to food to [the] bird[s] of the heavens and to [the] animal[s] of the earth.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
And I will make the city this into a waste and into a hissing every [one who] passes by at it he will be appalled and he may hiss on all wounds its.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
And I will make eat them [the] flesh of sons their and [the] flesh of daughters their and everyone [the] flesh of neighbor his they will eat in [the] siege and in [the] distress which they will press them enemies their and [those who] seek life their.
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
And you will break the bottle to [the] eyes of the men who go with you.
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
And you will say to them thus he says - Yahweh of hosts thus I will break the people this and the city this just as someone breaks [the] vessel of the potter which not it will be able to be repaired again and in Topheth people will bury from not room to bury.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
Thus I will do to the place this [the] utterance of Yahweh and to inhabitants its and to make the city this like Topheth.
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
And they will be [the] houses of Jerusalem and [the] houses of [the] kings of Judah like [the] place of Topheth the unclean [things] to all the houses which people made smoke on roofs their to all [the] host of the heavens and they poured out drink offerings to gods other.
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
And he came Jeremiah from Topheth where he had sent him Yahweh there to prophesy and he stood in [the] court of [the] house of Yahweh and he said to all the people.
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
Thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel here I ([am] about to bring *Q(k)*) to the city this and on all cities its all the calamity which I have spoken on it for they have stiffened neck their to not to hear words my.