< Irmiya 19 >
1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Thus saith Jehovah: Go and buy an earthen bottle of the potter, And take with thee the elders of the people, And the elders of the priests,
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
And go forth to the valley of the son of Hinnom, At the entrance of the pottery-gate, And proclaim there the words Which I shall speak to thee.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Say, Hear the word of Jehovah, Ye kings of Judah and inhabitants of Jerusalem! Thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Behold, I am about to bring such an evil upon this place, That whoever heareth of it, his ears shall tingle.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
For they have forsaken me, And have alienated this place, And have burned incense in it to strange gods, Which neither they, nor their fathers, nor the kings of Judah have known, And have filled this place with the blood of innocent children,
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
And have built high places to Baal, To burn their sons in the fire for burnt-offerings to Baal; Which I ordained not, and commanded not, And which never came into my mind.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
Therefore, behold, the days are coming, saith Jehovah, When this place shall no more be called Tophet, Nor the valley of the son of Hinnom, But the valley of Slaughter.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
For I will in this place bring to naught the plans of Judah and Jerusalem, And I will cause them to fall by the sword before their enemies, And by the hands of them that seek their lives; And their dead bodies will I give for food To the birds of heaven and the beasts of the earth.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
And I will make this city a wonder and a hissing; Every one that passeth by it shall wonder and hiss, On account of all its plagues.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
For I will cause them to eat the flesh of their sons and of their daughters, Yea, the flesh of each other shall they eat, In the straitness and the distress With which their enemies, and they that seek their lives, shall press them.
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
Then break thou the bottle Before the eyes of the men that go with thee.
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
And say to them: Thus saith Jehovah of hosts: So will I break this people and this city, As one breaks a potter's vessel which cannot be made whole again; And they shall be buried in Tophet, till there is no room to bury.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
Thus will I do to this place and to its inhabitants, saith Jehovah, And I will make this city itself like Tophet;
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
And the houses of Jerusalem and the houses of the kings of Judah shall be unclean, like the place of Tophet, All the houses upon whose roofs they have burned incense to all the host of heaven, And poured out drink-offerings to strange gods.
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Then came Jeremiah from Tophet, Whither Jehovah had sent him to prophesy, And stood in the court of the house of Jehovah, And said to all the people:
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
Thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Behold, I am about to bring upon this city, and upon all the cities belonging to it, All the evil which I have pronounced against it; For they have made their necks stiff, And refused to hearken to my words.