< Irmiya 19 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tafi ka sayo tulu a wurin mai ginin tukwane. Ka ɗauki waɗansu dattawan jama’a da kuma na firistoci
Thus says the Lord: “Go, and take a potter’s earthen bottle from the elders of the people and from the elders of the priests.
2 ku fita zuwa Kwarin Ben Hinnom, kusa da mashigin Ƙofar Kasko. A can ka furta maganganun da na faɗa maka,
And go out to the valley of the son of Hinnom, which is near the entrance to the earthen gate, and there you shall proclaim the words that I will speak to you.
3 ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
And you shall say: Listen to the word of the Lord, O kings of Judah, and you inhabitants of Jerusalem. Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Behold, I will lead an affliction over this place, so much so that it will ring in the ears of all who hear about it.
4 Gama sun yashe ni suka kuma mai da wannan wuri ya zama na baƙin alloli; sun ƙone hadayu a cikinsa wa allolin da ko su ko kakanninsu ko sarakunan Yahuda ba su taɓa sani ba, suka kuma cika wannan wuri da jini marasa laifi.
For they have abandoned me, and they have made this place foreign, and they have offered libations in it to foreign gods, whom neither they, nor their fathers, nor the kings of Judah have known. And they have filled this place with the blood of the innocent.
5 Suka gina masujadai na kan tudu na Ba’al don su ƙona’ya’yansu maza a cikin wuta a matsayin hadaya ga Ba’al abin da ban umarta ba, ban ambata ba, bai kuma zo mini ba.
And they have built the exalted places of Baal, in order to burn their children with fire as a holocaust to Baal, something that I did not instruct or speak of, nor did it enter into my heart.
6 Saboda haka ku lura, kwanaki suna zuwa, in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara ce da wannan wuri Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma za su ce da shi Kwarin Kisa.
Because of this, behold, the days are approaching, says the Lord, when this place will no longer be called Topheth, or the valley of the son of Hinnom, but the Valley of Slaughter.
7 “‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
And I will scatter the counsel of Judah and of Jerusalem in this place. And I will overthrow them with the sword, in the sight of their enemies and by the hand of those who seek their lives. And I will give their carcasses to the birds of the air and to the beasts of the land as food.
8 Zan ragargazar da wannan birni in mai da shi abin reni, duk wanda ya wuce zai yi mamaki ya kuma yi tsaki saboda dukan masifunsa.
And I will set this city amid stupor and hissing. Everyone who passes by it will be stupefied, and they will hiss over all its wounds.
9 Zan sa su ci naman’ya’yansu maza da mata, za su kuma ci naman juna a lokacin damuwar ƙawanya da abokan gāban da suke neman ransu za su yi musu.’
And I will feed them with the flesh of their sons and with the flesh of their daughters. And each one of them will eat the flesh of his friend during the blockade and the embargo by which their enemies, and those who seek their lives, will enclose them.
10 “Sa’an nan ka fasa tulun yayinda waɗanda suka tafi tare da kai suna duba,
And you shall crush the bottle in the sight of the men who will go with you.
11 ka kuma ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa zan farfasa wannan al’umma da wannan birni kamar yadda aka farfasa wannan tulu mai ginin tukwane ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne matattu a Tofet har sai ba sauran wuri.
And you shall say to them: Thus says the Lord of hosts: In the same way, I will crush this people and this city, just as the potter’s vessel was crushed and cannot be made whole again. And they will be buried at Topheth, because there will be no other place for burial.
12 Ga abin da zan yi wa wannan wuri da waɗanda suke zaune a nan, in ji Ubangiji. Zan mai da wannan birni kamar Tofet.
So will I do to this place and to its inhabitants, says the Lord. And I will make this city to be like Topheth.
13 Gidaje a Urushalima da waɗannan na sarakunan Yahuda za su ƙazantu kamar wannan wuri, Tofet, dukan gidajen da suke ƙone turare a kan rufi wa duk rundunan taurari suna kuma zuba hadayun sha ga sauran alloli.’”
And the houses of Jerusalem and the houses of the kings of Judah will be unclean, just like the place of Topheth: all the houses on whose roofs they sacrificed to all the armies of heaven and poured out libations to strange gods.”
14 Sa’an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don yă yi annabci, ya tsaya a filin haikalin Ubangiji ya ce wa mutane duka,
Then Jeremiah arrived from Topheth, where the Lord had sent him to prophesy, and he stood in the atrium of the house of the Lord, and he said to all the people:
15 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa wannan birni da ƙauyukan da suke kewayensa kowace masifar da na furta a kansu, domin sun yi taurinkai, ba su kuwa saurari maganata ba.’”
“Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Behold, I will lead over this community, and over all its cities, all the evils that I have spoken against it. For they have hardened their necks, so that they would not heed my words.”

< Irmiya 19 >