< Irmiya 18 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Dette er det ord som kom til Jeremias fra Herren:
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Stå op og gå ned til pottemakerens hus, og der vil jeg la dig høre mine ord.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
Og jeg gikk ned til pottemakerens hus, og se, han gjorde sitt arbeid på skiven;
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
og når det kar han gjorde, blev mislykket, som det kan gå med leret i pottemakerens hånd, så gjorde han det om igjen til et annet kar, slik som han vilde ha det.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
Skulde jeg ikke kunne gjøre med eder, Israels hus, som denne pottemaker? sier Herren; se, som leret er i pottemakerens hånd, således er I i min hånd, Israels hus!
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
En gang taler jeg om et folk og et rike, at jeg vil rykke op og rive ned og ødelegge;
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
men dersom det folk som jeg har talt om, vender om fra sin ondskap, da angrer jeg det onde som jeg hadde tenkt å gjøre mot det.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
Og en annen gang taler jeg om et folk og om et rike, at jeg vil bygge og plante;
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
men gjør det da det som er ondt i mine øine, så det ikke hører på min røst, da angrer jeg det gode som jeg hadde tenkt å ville gjøre mot det.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
Og si nu til Judas menn og til Jerusalems innbyggere: Så sier Herren: Se, jeg emner på en ulykke for eder og uttenker et ondt råd mot eder; vend om, hver fra sin onde vei, og bedre eders veier og eders gjerninger!
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
Men de sier: Du taler forgjeves! Våre egne tanker vil vi følge, og enhver av oss vil følge sitt onde, hårde hjerte.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Derfor sier Herren så: Spør blandt hedningefolkene: Hvem har hørt slikt? Grufulle ting har jomfruen Israel gjort.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Mon Libanons sne går bort på det høie fjell? Eller uttørkes de fremmede, kjølige, rinnende vann?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Men mitt folk har glemt mig, det brenner røkelse for de falske guder; og de førte dem til fall på deres veier, de gamle veier, så de gikk på stier, på uryddede veier,
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
og således gjorde de sitt land til en forferdelse, til en evig spott; hver den som går forbi, skal forferdes og ryste på hodet.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Som østenvinden vil jeg adsprede dem for fiendens åsyn; med nakken og ikke med ansiktet vil jeg se på dem på deres ulykkes dag.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
Da sa de: Kom og la oss uttenke onde råd mot Jeremias! For presten har jo loven, den vise har råd, og profeten har ord fra Gud. Kom, la oss slå ham med tungen og ikke akte på noget av hans ord!
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Akt på mig, Herre, og hør hvorledes de strider mot mig!
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Skal en gjengjelde godt med ondt? For de har gravd en grav for mitt liv. Kom i hu at jeg stod for ditt åsyn og talte godt for dem for å vende din vrede bort fra dem!
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Gi derfor deres barn til hungeren, og overgi dem selv i sverdets vold, og la deres hustruer bli barnløse og enker, og deres menn bli drept av pesten, deres ungdom bli slått ihjel av sverdet i krigen!
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
La skrik bli hørt fra deres hus, når du lar en fiendeskare komme brått over dem! For de har gravd en grav for å fange mig og lagt skjulte snarer for mine føtter.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Men du, Herre, kjenner alle deres onde råd mot mitt liv; forlat dem ikke deres misgjerning og utslett ikke deres synd for ditt åsyn, men styrt dem ned for ditt åsyn! Straff dem på din vredes tid!