< Irmiya 18 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
The word which it came to Jeremiah from with Yahweh saying.
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Arise and you will go down [the] house of the potter and there I will cause to hear you words my.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
And I went down [the] house of the potter (and there! he *Q(K)*) [was] doing work on the stones.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
And it was spoiled the vessel which he [was] making with the clay in [the] hand of the potter and he would return and he made it a vessel another just as it was pleasing in [the] eyes of the potter to do.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
¿ Like the potter this not am I able to do to you O house of Israel [the] utterance of Yahweh here! like the clay in [the] hand of the potter so you [are] in hand my O house of Israel.
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
A moment I will speak on a nation and on a kingdom to pluck up and to pull down and to destroy.
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
And it will turn away the nation that from evil its which I had spoken on it and I will relent on the calamity which I had planned to do to it.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
And a moment I will speak on a nation and on a kingdom to build up and to plant.
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
And it will do (the evil *Q(K)*) in view my to not to listen to voice my and I will relent on the good which I had said to do good to it.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
And therefore say please to everyone of Judah and to [the] inhabitants of Jerusalem saying thus he says Yahweh here! I [am] about to fashion on you calamity and [am] about to plan on you a plan turn back please everyone from way his wicked and make good ways your and deeds your.
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
And they say despairing for after own plans our we will walk and everyone [the] stubbornness of heart his wicked we will act.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Therefore thus he says Yahweh ask please among the nations who? has he heard like these [things] a horrible [thing] she has done exceedingly [the] virgin of Israel.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
¿ Does it leave from [the] rock of [the] field [the] snow of Lebanon or? are they plucked up waters strange cool flowing.
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
For they have forgotten me people my to falsehood they make smoke and they have caused to stumble them in ways their paths of antiquity to walk paths a way not built up.
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
To make land their into a waste (whistling of *Q(K)*) perpetuity every [one who] passes by at it he will be appalled and he may wag with head his.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Like a wind of [the] east I will scatter them before an enemy back and not face I will show them on [the] day of disaster their.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
And people said come so let us plan on Jeremiah plans for not it will be lost instruction from [the] priest and counsel from [the] wise and word from [the] prophet come and let us attack him with the tongue and may not we pay attention to all words his.
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Be attentive! O Yahweh to me and listen to [the] voice of opponents my.
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
¿ Will it be repaid in place of good evil for they have dug a pit for self my remember - standing my before you to speak on them good to turn back rage your from them.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Therefore give children their to famine and pour them over [the] hands of [the] sword so they may become wives their childless and widows and men their may they be [the] slain of death young men their [those] struck down of [the] sword in battle.
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
May it be heard a cry of distress from houses their if you will bring on them a marauding band suddenly for they have dug (a pit *Q(K)*) to capture me and snares they have hidden for feet my.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
And you O Yahweh you know all plan their on me for death may not you atone on iniquity their and sin their from to before you may not you wipe out (and let them be *Q(K)*) overthrown before you in [the] time of anger your do with them.