< Irmiya 18 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
The word that came unto Jeremiah from Yahweh, saying:
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Arise and go down to the house of the potter, —and, there, will I cause thee to hear my words.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
So I went down, to the house of the potter, —and there he was! making a piece of work on the wheels,
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
Then was marred, the vessel that he was making, while yet it was clay in the hand of the potter, —so he turned and made of it another vessel, as seemed right in the eyes of the potter to make it.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then came the word of Yahweh unto me, saying:
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
Like this potter, can I not deal with you O house of Israel? Demandeth Yahweh: Lo! as clay in the hand of the potter, So, are, ye, in my hand O house of Israel.
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
The moment I speak, concerning a nation or concerning a kingdom, —to pull up and to break down, and to destroy;
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
and that nation return from its wickedness against whom I have spoken, then will I repent concerning the calamity which I had devised to bring upon it.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
And, the moment I speak, concerning a nation or concerning a kingdom, —to build and to plant;
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
and it commit wickedness in mine eyes, in not hearkening unto my voice, then will I repent concerning the good wherewith I had said I would do it good.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
Now, therefore, I pray thee, speak unto the men of Judah and concerning the inhabitants of Jerusalem saying, Thus, saith Yahweh, —Lo! I am fashioning against you calamity, and devising against you, a device, —Return I pray you every man from his wicked way, And amend your ways and your doings.
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
And, since they will say, Hopeless! For after our own devices, will we walk, And, every one, the stubbornness of his own wicked heart, will we do!
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Therefore, Thus saith Yahweh, Ask I pray you among the nations, —Who hath heard such things as these? A very horrible thing, hath, the virgin, Israel done!
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Shall the snow of Lebanon, fail from the rock of the field? Or shall waters from afar, deep, overflowing, be dried up?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Yet my people have forgotten me, Unto vanity, have they been burning incense; And it hath caused them to stumble In their ways The roads of age-past times, To walk in by-paths—A way not cast up.
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
To make their land a desolation The hissings of age-abiding times, —Every one that passeth by her, shall be astonished and wag his head.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Like an east wind, will I scatter them before the enemy, —The back and not the face, will I let them see in the day of their distress.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
Then said they, —Come ye and let us devise against Jeremiah devices, For the law shall not perish from the priest, Nor, counsel, from the wise, Nor, the word from the prophet: Come and let as smite him with the tongue, And let us not give ear to any of his words!
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Give thou ear O Yahweh unto me, —And hearken unto the voice of mine accusers.
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Shall, evil, be recompensed for good? For they have digged a pit for my life, —Remember how I stood before thee To speak in their behalf what was good! To turn back thine indignation from them.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Therefore, give thou up their sons to the famine And deliver them into the hands of the sword, And let their, wives, become, childless and widows, And let, their men, be slain by death, Their young men be smitten by the sword in battle.
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Let there be heard a cry out of their houses, When thou shalt bring in upon them a troop, suddenly, —Because they digged a pit to capture me, And snares, did they hide for my feet.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
But, thou, O Yahweh, knowest all their counsels against me to put me to death, Put thou no propitiatory-covering over their iniquity, And their sin from before thee, do not thou blot out, —But let them be overthrown before thee, In the time of thine anger, deal thou effectively with them.