< Irmiya 18 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
The word which came to Jeremiah from Jehovah, saying:
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Arise, and go down to the potter's house, and there will I cause thee to hear my words.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
So I went down to the potter's house, and behold, he was at work at the wheel.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
And the vessel which he was making of clay was marred in the hand of the potter; so he began anew and made it another vessel, as seemed good to the potter to make it.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then came the word of Jehovah to me, saying:
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
Cannot I do after the manner of this potter With respect to you. O house of Israel, saith Jehovah? Behold, as the clay is in the hand of the potter, So are ye in my hand, O house of Israel!
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
Whenever I speak concerning a nation or a kingdom, That I will pluck it up, cast it down, or destroy it,
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
If that nation shall turn from its wickedness On account of which I threatened it, Then will I repent of the evil which I purposed to do to it.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
And whenever I speak concerning a nation or a kingdom, That I will build it, or plant it,
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
And it shall do that which is evil in my sight, And not hearken to my voice, Then will I repent of the good with which I promised to bless them.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
And now speak to the men of Judah, And to the inhabitants of Jerusalem, saying, Thus saith Jehovah: Behold, I am framing evil against you, And meditating a design against you; Return ye now every one from his evil way, And amend your ways and your doings.
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
But they say, “There is no remedy, For we will walk after our own devices, And we will practise every one the perverseness of his evil heart.”
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Therefore thus saith Jehovah: Inquire ye now among the nations, Who hath heard such things as these? The virgin of Israel hath done a deed of horror.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Shall the snow from the rocks of Lebanon forsake my fields? Or shall the cold flowing waters, that come from afar, be dried up?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Yet my people have forgotten me, And burned incense to vanity; They stumble in their paths, the old ways, And walk in ways that have not been thrown up,
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
To make their land a desolation, A perpetual hissing; Every one that passeth through it shall be amazed, And shake his head.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
I will scatter them before the enemy, as with the east wind; I will show them the back, and not the face, In the day of their calamity.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
But they say, “Come, let us devise measures against Jeremiah; For the law shall not perish from the priest, Nor counsel from the wise, Nor the word from the prophet; Come, let us smite him with the tongue, And not give heed to any of his words.”
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Give heed to me, O Jehovah, And hear the voice of my adversaries!
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Shall evil be returned for good? For they have digged a pit for me. Remember how I have stood before thee, To announce good to them, And to turn away thy wrath from them!
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Therefore give thou up their sons to famine, And deliver them to the edge of the sword! Let their wives be childless and widows, Let their men be slain by pestilence, And their young men fall by the sword in battle!
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Let a cry be heard from their houses, When thou shalt bring a troop upon them suddenly! For they have digged a pit to take me, And hidden snares for my feet.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Thou, O Jehovah, knowest all their plots against my life! Cover not their iniquity, And blot not out their sin from thy sight! But let them be overthrown before thee; Deal with them in the time of thy wrath!