< Irmiya 18 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
The word which came to Jeremiah from the Lord, saying,
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Arise, and go down to the potter's house, and there will I let thee hear my words.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
Then went I down to the potter's house, and, behold, he was doing work on the wheels.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
And the vessel that he was making became spoiled as [happeneth] with the clay in the hand of the potter; and he made again thereof another vessel, as it seemed good in the eyes of the potter to make it.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then came the word of the Lord to me, saying,
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
Shall I not be able to do unto you as this potter, O house of Israel? saith the Lord. Behold, as the clay is in the potter's hand, so are ye in my hand, O house of Israel.
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
At one instant I speak concerning a nation, and concerning a kingdom, to root out, and to pull down, and to destroy it;
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
But should that nation, against whom I have spoken, return from their wrong-doing: then will I bethink me of the evil that I had thought to do unto them.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
And at one instant I speak concerning a nation, and concerning a kingdom, to build and to plant it;
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
But should it do what is evil in my eyes, so as not to hearken to my voice: then will I bethink me of the good, wherewith I had thought to benefit the same.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
And now do say to the men of Judah, and to the inhabitants of Jerusalem, as followeth, Thus hath said the Lord, Behold, I form against you evil, and devise against you a device: do but return now every one from his evil way, and amend your ways and your deeds.
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
And they said, It is useless: for after our own thoughts will we walk, and we will every one do after the stubbornness of his evil heart.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Therefore thus hath said the Lord, Only ask among the nations, Who hath heard the like things? a very horrible act hath the virgin of Israel committed.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Doth the snow of Lebanon ever quit the rock of the field? or do the far-coming, cold, flowing waters ever fail?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
That my people have forgotten me, that they have burnt incense to false gods, and are made to stumble on their ways, the ancient beaten tracks, to walk in paths, on a road which is not leveled?
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
To make their land desolate, a perpetual derision: every one that passeth thereby shall be astonished, and shake his head.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Like an east wind will I scatter them before the enemy; with the back, and not the face, will I regard them on the day of their calamity.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
And they said, Come, and let us contrive devices against Jeremiah; for the law will not be lost from the priest, nor counsel from the wise, nor the word from the prophet. Come, and let us smite him with the tongue, and let us not listen to any of his words.
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Listen to me, O Lord, and hearken to the voice of those that contend with me.
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Shall evil be recompensed instead of good, that they have dug a pit for my life? Remember my standing before thee to speak good concerning them, to cause thy wrath to turn away from them.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Therefore give up their children to the famine, and let their life ebb out by means of the sword; and let their wives be bereaved of their children, and widows; and let their men be slain by death; their young men smitten by the sword in the battle.
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Let a cry be heard from their houses, when thou bringest a troop over them suddenly; for they have dug a pit to catch me, and laid concealed snares for my feet.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Yet thou, Lord, knowest well all their counsel against me to [procure my] death: forgive not their iniquity, and let their sin not be blotted out from before thee; but let them be brought to stumbling before thee; in the time of thy anger deal thus with them.