< Irmiya 17 >
1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
»Judov greh je zapisan z železnim peresom in z diamantno konico. Ta je vrezan na ploščo njihovega srca in na rogove njihovih oltarjev,
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
medtem ko se njihovi otroci spominjajo njihovih oltarjev in njihovih ašer pri zelenih drevesih na visokih hribih.
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
Oh moja gora na polju, tvoje imetje in vse tvoje zaklade bom izročil v plen in tvoje visoke kraje zaradi greha, po vseh tvojih mejah.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
Ti pa, celo ti sam, boš odpravljen od svoje dediščine, ki sem ti jo dal in povzročil ti bom, da služiš svojim sovražnikom v deželi, ki je ne poznaš, kajti zanetili ste ogenj v moji jezi, ki bo gorel na veke.«
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Tako govori Gospod: »Preklet bodi človek, ki zaupa v moža in postavlja osebo [za] svoj laket in katerega srce odhaja od Gospoda.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
Kajti podoben bo brinu v puščavi in ne bo videl, ko prihaja dobro, temveč bo naselil izsušene kraje v divjini, v slani in nenaseljeni deželi.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Blagoslovljen je človek, ki zaupa v Gospoda in čigar upanje je v Gospodu.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
Kajti on bo kakor drevo, posajeno ob vodah in ki razširja svoje korenine ob reki in ne bo videlo, ko prihaja vročina, temveč bo njegovo listje zeleno; v sušnem letu ne bo zaskrbljeno niti ne bo prenehalo rojevati sadu.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
Srce je varljivo nad vsemi stvarmi in obupno zlobno. Kdo ga lahko spozna?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
Jaz, Gospod, preiskujem srce, jaz preizkušam notranjost, celó da vsakemu človeku dam glede na njegove poti in glede na sad njegovih dejanj.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
Kakor jerebica sedi na jajcih, ki jih ni znesla, tako tisti, ki pridobiva bogastva, pa ne po pravici, jih bo zapustil v sredi svojih dni in ob svojem koncu bo bedak.«
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
Veličasten visok prestol od začetka je prostor našega svetišča.
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
Oh Gospod, Izraelovo upanje, vsi, ki te zapustijo, bodo osramočeni in tisti, ki odidejo od mene, bodo zapisani v zemljo, ker so zapustili Gospoda, studenec živih vodá.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Ozdravi me, oh Gospod in jaz bom ozdravljen, reši me in jaz bom rešen, kajti ti si moja hvala.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Glej, pravijo mi: »Kje je beseda od Gospoda? Naj ta sedaj pride.«
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
Kar se mene tiče, nisem hitel pred tem, da bi bil pastir, da ti sledim. Niti si nisem želel dneva, polnega gorja; ti veš. To, kar je prišlo iz mojih ustnic, je bilo pred teboj pravilno.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Ne bodi mi strahota. Ti si moje upanje v dnevu zla.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Naj bodo zbegani [tisti], ki me preganjajo, toda jaz naj ne bom zbegan. Naj bodo zaprepadeni, toda jaz naj ne bom zaprepaden. Nanje privedi dan zla in jih uniči z dvojnim uničenjem.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Tako mi je rekel Gospod: »Pojdi in stoj v velikih vratih otrok ljudstva, pri katerih Judovi kralji vstopajo in pri katerih gredo ven in v vseh jeruzalemskih velikih vratih
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
in jim reci: ›Poslušajte Gospodovo besedo, vi Judovi kralji in ves Juda in vsi prebivalci Jeruzalema, ki vstopate pri teh velikih vratih.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Tako govori Gospod: ›Pazite nase in na šabatni dan ne prenašajte nobenega bremena niti tega ne prinašajte noter pri jeruzalemskih velikih vratih.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
Niti ne prinašajte bremena iz svojih hiš na šabatni dan niti ne počnite nobenega dela, temveč posvečujte šabatni dan, kakor sem zapovedal vašim očetom.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
Toda niso ubogali niti niso nagnili svojega ušesa, temveč so otrdili svoj vrat, da ne bi niti slišali niti prejeli poučevanja.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
In zgodilo se bo, če mi boste marljivo prisluhnili, ‹ govori Gospod, ›da ne prinašate nobenega bremena skozi velika vrata tega mesta na šabatni dan, temveč posvečujete šabatni dan, da v tem [dnevu] ne delate nobenega dela,
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
potem bodo tam, v velika vrata tega mesta, vstopali kralji in princi, sedeč na Davidovem prestolu, jahajoč na bojnih vozovih in konjih, oni in njihovi princi, Judovi možje in prebivalci Jeruzalema; in to mesto bo ostalo na veke.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
Prišli bodo iz Judovih mest in iz krajev okoli Jeruzalema in iz Benjaminove dežele in ravnine in z gora in iz juga, prinašajoč žgalne daritve, klavne daritve, jedilne daritve in kadilo ter prinašajoč daritve hvale v Gospodovo hišo.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
Toda če mi ne boste prisluhnili, da posvečujete šabatni dan in da ne nosite bremena, celo ko vstopate pri jeruzalemskih velikih vratih na šabatni dan, potem bom zanetil ogenj v njegovih velikih vratih in ta bo požrl jeruzalemske palače in ne bo pogašen.‹«