< Irmiya 17 >

1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
Le péché de Juda a été écrit avec une plume de fer et avec une pointe de diamant, et gravé sur l’étendue de leur cœur et sur les cornes de leurs autels.
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
Puisque leurs fils se sont souvenus de leurs autels, et de leurs bois sacrés, et des arbres couverts de feuilles, sur les montagnes élevées,
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
Offrant des sacrifices dans la campagne, j’abandonnerai au pillage ta force et tous tes trésors, et tes hauts lieux à cause de tes péchés commis dans tous tes confins.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
Et tu seras laissée seule privée de ton héritage que je t’ai donné, et je te rendrai l’esclave de tes ennemis dans une terre que tu ignores, parce que tu as allumé un feu dans ma fureur; jusqu’à jamais il brûlera.
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Voici ce que dit le Seigneur: Maudit l’homme qui se confie dans l’homme, qui se fait un bras de chair, et dont le cœur se retire du Seigneur.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
Il sera comme le tamaris qui est dans le désert et il ne verra pas le bonheur, lorsqu’il viendra; mais il habitera dans la sécheresse au désert, dans une terre de salure et inhabitable.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Béni l’homme qui se confie dans le Seigneur, et dont le Seigneur sera l’espérance.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
Et il sera comme un arbre que l’on transplante sur le bord des eaux, qui étend ses racines vers l’eau qui l’humecte; il ne craindra pas la chaleur, lorsqu’elle viendra. Et sa feuille sera verte, et au temps de la sécheresse il ne sera pas en peine, et jamais il ne cessera de faire du fruit.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
Le cœur de tous est dépravé et inscrutable; qui le connaîtra?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
C’est moi, le Seigneur qui scrute le cœur, et qui éprouve les reins; qui donne à chacun selon sa voie et selon le fruit de ses inventions.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
La perdrix a couvé des œufs qu’elle n’a pas pondus, ainsi l’injuste a amassé des richesses, mais non avec justice; au milieu de ses jours il abandonnera ses richesses, et à son dernier moment, il sera reconnu insensé.
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
Le trône de gloire, élevé depuis le commencement, est le lieu de notre sanctification.
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
Seigneur, l’attente d’Israël, tous ceux qui vous abandonnent seront confondus; ceux qui se retirent de vous seront écrits sur la terre, parce qu’ils ont abandonné la source des eaux vives, le Seigneur.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Guérissez-moi, Seigneur, et je serai guéri; sauvez-moi, et je serai sauvé; parce que ma louange, c’est vous.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Voilà qu’eux-mêmes me disent: Où est la parole du Seigneur? qu’elle vienne.
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
Et moi je n’ai pas été troublé, en vous suivant comme pasteur; et le jour d’un homme, je ne l’ai pas désiré, vous le savez. Ce qui est sorti de mes lèvres a été juste en votre présence.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Ne me soyez pas à effroi, mon espoir, c’est vous, au jour de l’affliction.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Qu’ils soient confondus, ceux qui me persécutent, et que je ne sois pas confondu moi-même; qu’ils tremblent de peur, eux, et que je ne tremble pas moi-même; amenez sur eux un jour d’affliction, et d’un double brisement, brisez-les.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Voici ce que me dit le Seigneur: Va, et tiens-toi à la porte des fils du peuple, par laquelle les rois de Juda entrent et sortent, et à toutes les portes de Jérusalem;
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
Et tu leur diras: Ecoutez la parole du Seigneur, rois de Juda, tout Juda, et vous tous, habitants de Jérusalem, qui entrez par ces portes.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Voici ce que dit le Seigneur: Gardez vos âmes, ne portez point de fardeaux au jour du sabbat, et n’en introduisez point par les portes de Jérusalem.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
Et ne faites pas sortir de fardeaux hors de vos maisons au jour du sabbat, et vous ne ferez aucun travail; mais sanctifiez le jour du sabbat comme je l’ai ordonné à vos pères.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
Et ils n’ont pas entendu, et ils n’ont pas incliné leur oreille; mais ils ont rendu leur cou inflexible, afin de ne pas m’entendre, et de ne pas recevoir mes instructions.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
Et il arrivera que si vous m’écoutez, dit le Seigneur, en sorte que vous n’introduisiez point de fardeaux par les portes de cette ville au jour du sabbat, et si vous sanctifiez le jour du sabbat, si vous ne faites en ce jour aucun travail,
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
Il entrera par les portes de cette ville des rois et des princes qui s’assiéront sur le trône de David, qui seront montés sur leurs chars et sur leurs chevaux, eux et leurs princes, et les hommes de Juda, et les habitants de Jérusalem; et cette ville sera habitée éternellement.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
Et ils viendront des villes de Juda, et des environs de Jérusalem, et de la terre de Benjamin, et des plaines, et des montagnes, et du midi, portant des holocaustes et des victimes, des sacrifices et de l’encens, et ils les apporteront en offrande dans la maison du Seigneur.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
Mais si vous ne m’écoutez pas, si vous ne sanctifiez pas le jour du sabbat, en ne portant point de fardeaux, et n’en introduisant point par les portes de Jérusalem au jour du sabbat, je mettrai le feu à ses portes; et il dévorera les maisons de Jérusalem, et il ne s’éteindra pas.

< Irmiya 17 >