< Irmiya 17 >

1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
Le péché de Juda est écrit avec un burin d’acier de fer, [et] avec une pointe de diamant; il est gravé sur la table de leur cœur, et aux cornes de leurs autels.
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
De sorte que leurs fils se souviendront de leurs autels, et de leurs bocages, auprès des arbres verts sur les hautes collines.
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
Montagnard, je livrerai par les champs tes richesses [et] tous tes trésors au pillage; tes hauts lieux [sont pleins] de péché dans toutes tes contrées.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
Et toi, et [ceux qui sont] avec toi, vous laisserez vacant l'héritage que je t'avais donné, et je ferai que tu seras asservi à tes ennemis, dans un pays que tu ne connais point, parce que vous avez allumé le feu en ma colère; [et] il brûlera à toujours.
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Ainsi a dit l'Eternel: maudit soit l'homme qui se confie en l'homme, et qui fait de la chair son bras, et dont le cœur se retire de l'Eternel.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
Car il sera comme la bruyère en une lande, et il ne s'apercevra point quand le bien sera venu; mais il demeurera au désert en des lieux secs, en une terre salée et inhabitable.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Béni soit l'homme qui se confie en l'Eternel, et duquel l'Eternel est la confiance.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
Car il sera comme un arbre planté près des eaux, et qui étend ses racines le long d'une eau courante; quand la chaleur viendra, il ne s'en apercevra point; et sa feuille sera verte, il ne sera point en peine en l'année de la sécheresse, et ne cessera point de porter du fruit.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
Le cœur est rusé, et désespérément malin par dessus toutes choses; qui le connaîtra?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
Je suis l'Eternel, qui sonde le cœur, et qui éprouve les reins; même pour rendre à chacun selon sa voie, [et] selon le fruit de ses actions.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
Celui qui acquiert des richesses, sans observer la justice, est une perdrix [qui] couve ce qu'elle n'a point pondu; il les laissera au milieu de ses jours, et à la fin il sera trouvé insensé.
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
Le lieu de notre Sanctuaire est un trône de gloire, un lieu haut élevé dès le commencement.
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
Eternel, qui es l'attente d'Israël, tous ceux qui t'abandonnent seront honteux; ceux qui se détournent de moi, seront écrits en la terre, parce qu'ils ont délaissé la source des eaux vives, l'Eternel.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Eternel, guéris-moi, et je serai guéri; sauve-moi, et je serai sauvé; car tu es ma louange.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Voici, ceux-ci me disent: où est la parole de l'Eternel? qu'elle vienne présentement!
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
Mais je ne me suis point avancé plus qu'un pasteur après toi, et je n'ai point désiré le jour de l'extrême affliction, tu le sais; et ce qui est sorti de mes lèvres a été devant toi.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Ne me sois point en effroi, tu es ma retraite au jour du mal.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Que ceux qui me persécutent soient honteux, mais que je ne sois point honteux; qu'ils soient épouvantés, mais que je ne sois point épouvanté; amène sur eux le jour du mal, et les accable d'une double plaie.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Ainsi m'a dit l'Eternel: va, et tiens-toi debout à la porte des enfants du peuple, par laquelle les Rois de Juda entrent, et par laquelle ils sortent; et à toutes les portes de Jérusalem.
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
Et leur dis: écoutez la parole de l'Eternel, Rois de Juda, et vous tous [hommes] de Juda, et vous tous habitants de Jérusalem qui entrez par ces portes;
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Ainsi a dit l'Eternel: prenez garde à vos âmes, et ne portez aucun fardeau le jour du Sabbat, et ne les faites point passer par les portes de Jérusalem.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
Et ne tirez point hors de vos maisons aucun fardeau le jour du Sabbat, et ne faites aucune œuvre, mais sanctifiez le jour du Sabbat, comme j'ai commandé à vos pères.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
Mais ils n'ont point écouté, et n'ont point incliné leur oreille, mais ils ont raidi leur cou, pour n'écouter point, et pour ne recevoir point d'instruction.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
Il arrivera donc si vous m'écoutez attentivement, dit l'Eternel pour ne faire passer aucun fardeau par les portes de cette ville le jour du Sabbat, et si vous sanctifiez le jour du Sabbat, tellement que vous ne fassiez aucune œuvre en ce jour-là;
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
Que les Rois et les principaux, ceux qui sont assis sur le trône de David, montés sur des chariots et sur des chevaux, eux et les principaux d'entre eux, les hommes de Juda, et les habitants de Jérusalem, entreront par les portes de cette ville; et cette ville sera habitée à toujours.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
On viendra aussi des villes de Juda, et des environs de Jérusalem et du pays de Benjamin, et de la campagne, et des montagnes, et de devers le Midi, et on apportera des holocaustes, des sacrifices, des oblations et de l'encens; on apportera aussi [des sacrifices] d'action de grâces en la maison de l'Eternel.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
Mais si vous ne m'écoutez point pour sanctifier le jour du Sabbat, et pour ne porter aucun fardeau, et n'en faire entrer aucun par les portes de Jérusalem le jour du Sabbat, je mettrai le feu à ses portes, il consumera les palais de Jérusalem, et ne sera point éteint.

< Irmiya 17 >