< Irmiya 17 >

1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
[the] sin of Judah [is] inscribed with a stylus of iron with a point of flint [is] engraved on [the] tablet of heart their and to [the] horns of altars your.
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
When remember children their altars their and Asherah poles their at tree[s] luxuriant on hills high.
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
Mountain my in the field wealth your all treasures your to plunder I will give high places your for sin in all territories your.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
And you will let fall and in you from inheritance your which I gave to you and I will make serve you enemies your in land which not you know for a fire you have kindled in anger my until perpetuity it will burn.
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Thus - he says Yahweh [is] cursed the man who he trusts in humankind and he makes flesh strength his and from Yahweh it turns aside heart his.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
And he will be like a bush in the desert plain and not he will see if it will come good and he will dwell parched places in the wilderness a land of saltiness and not anyone dwells.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
[is] blessed The man who he trusts in Yahweh and he is Yahweh trust his.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
And he will be like a tree - planted at water and [which] at a stream it sends out roots its and not (he will see *Q(K)*) if it will come heat and it will be leafage its luxuriant and in a year of drought not it will be anxious and not it will cease from producing fruit.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
[is] deceitful The heart more than everything and [is] incurable it who? will he know it.
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
I Yahweh [am] searching [the] heart [am] testing [the] kidneys to give to everyone (according to ways his *Q(K)*) according to [the] fruit of deeds his.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
A partridge [which] it gathers a brood and not it has laid [one who] makes wealth and not with justice in [the] middle of (days his *Q(K)*) it will leave him and at end his he will be a fool.
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
[is] a throne of Glory a high place from first [time] [the] place of sanctuary our.
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
O hope of Israel O Yahweh all [those who] forsake you they will be ashamed (and disloyal [ones] my *Q(K)*) in the land they will be written down for they have forsaken [the] spring of water living Yahweh.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Heal me O Yahweh so I may be healed save me so let me be saved for [are] praise my you.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Here! they [are] saying to me where? [is] [the] word of Yahweh let it come please.
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
And I not I have hastened - from a shepherd after you and a day incurable not I have desired you you know [the] utterance of lips my before face your it was.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
May not you become to me an object of terror [are] refuge my you in a day of calamity.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Let them be put to shame pursuers my and may not I be put to shame I let them be dismayed they and may not I be dismayed I bring on them a day of calamity and double destruction destroy them.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Thus he said Yahweh to me go and you will stand in [the] gate of [the] sons of (the people *Q(K)*) which they go in it [the] kings of Judah and which they go out in it and in all [the] gates of Jerusalem.
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
And you will say to them hear [the] word of Yahweh O kings of Judah and all Judah and all [the] inhabitants of Jerusalem who go in the gates these.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Thus he says Yahweh take heed to lives your and may not you carry a burden on [the] day of the sabbath and you will bring [it] in [the] gates of Jerusalem.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
And not you must bring out a burden from houses your on [the] day of the sabbath and any work not you must do and you will set apart as holy [the] day of the sabbath just as I commanded ancestors your.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
And not they listened and not they inclined ear their and they stiffened neck their to not (to listen *Q(K)*) and to not to accept correction.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
And it will be certainly [if] you will listen! to me [the] utterance of Yahweh to not - to bring a burden in [the] gates of the city this on [the] day of the sabbath and to set apart as holy [the] day of the sabbath to not to do (on it *Q(K)*) any work.
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
And they will come in [the] gates of the city this kings - and princes [who] sit on [the] throne of David [who] ride - in chariot[s] and on horses they and officials their everyone of Judah and [the] inhabitants of Jerusalem and it will remain the city this for ever.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
And they will come from [the] cities of Judah and from round about Jerusalem and from [the] land of Benjamin and from the Shephelah and from the hill country and from the Negev [those who] bring burnt offering and sacrifice and grain offering and frankincense and [those who] bring a thank-offering [the] house of Yahweh.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
And if not you will listen to me to set apart as holy [the] day of the sabbath and to not - to carry a burden and to go in [the] gates of Jerusalem on [the] day of the sabbath and I will kindle a fire in gates its and it will consume [the] fortresses of Jerusalem and not it will be extinguished.

< Irmiya 17 >