< Irmiya 17 >

1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
“The sin of Judah is written with a pen of iron, With the point of a diamond, Engraved on the tablet of their heart, And on the horns of your altars,
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
As their sons remember their altars and their Asherim, By the green tree, by the high hills.
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
O My mountain in the field—your strength, All your treasures—I give for a prey, Your high places for sin in all your borders.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
And you have let go—even through yourself, Of your inheritance that I gave to you, And I have caused you to serve your enemies, In a land that you have not known, For you have kindled a fire in My anger, It burns for all time.”
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Thus said YHWH: “Cursed [is] the man who trusts in man, And has made flesh his arm, And whose heart turns from YHWH.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
And he has been as a naked thing in a desert, And does not see when good comes, And has inhabited parched places in a wilderness, A salt land, and not inhabited.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Blessed [is] the man who trusts in YHWH, And whose confidence has been YHWH.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
And has been as a tree planted by waters, And he sends forth his roots by a stream, And he does not see when heat comes, And his leaf has been green, And he is not sorrowful in a year of scarcity, Nor does he cease from making fruit.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
The heart [is] deceitful above all things, And it [is] incurable—who knows it?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
I, YHWH, search the heart, try the reins, Even to give to each according to his way, According to the fruit of his doings.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
A partridge hatching, and not bringing forth, [Is] one making wealth, and not by right, In the midst of his days he forsakes it, And in his latter end—he is a fool.”
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
A throne of glory on high from the beginning, The place of our sanctuary,
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
The hope of Israel [is] YHWH, All forsaking You are ashamed. “And My apostates are written in the earth, For they have forsaken YHWH, A fountain of living waters.”
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Heal me, O YHWH, and I am healed, Save me, and I am saved, For You [are] my praise.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Behold, they are saying to me: “Where [is] the word of YHWH? Pray, let it come.”
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
And I did not hurry from feeding after You, And I have not desired the desperate day, You have known the produce of my lips, It has been before Your face,
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Do not be to me for a terror, You [are] my hope in a day of calamity.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Let my pursuers be ashamed, And do not let me be ashamed—me! Let them be frightened, And do not let me be frightened—me! Bring in on them a day of calamity, And destroy them a second time [with] destruction.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Thus said YHWH to me: “Go, and you have stood in the gate of the sons of the people, by which kings of Judah come in, and by which they go out, and in all gates of Jerusalem,
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
and you have said to them: Hear a word of YHWH, you kings of Judah, and all Judah, and all inhabitants of Jerusalem, who are coming in by these gates,”
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Thus said YHWH: “Take heed to yourselves, And you do not bear a burden on the day of rest, Nor have you brought [it] in by the gates of Jerusalem.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
Nor do you take out a burden from your houses on the day of rest, Indeed, you do not do any work, And you have sanctified the day of rest, As I have commanded your fathers.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
And they have not listened nor inclined their ear, And they stiffen their neck not to hear, And not to receive instruction.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
And it has been, if you certainly listen to Me,” A declaration of YHWH, “So as not to bring in a burden by the gates of this city on the day of rest, And to sanctify the day of rest, So as not to do any work in it—
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
Then kings and princes have entered by the gates of this city, Sitting on the throne of David, Riding in a chariot, and on horses, They, and their princes, the man of Judah, And inhabitants of Jerusalem, And this city has remained for all time.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
And they have come in from cities of Judah, And from outskirts of Jerusalem, And from the land of Benjamin, And from the low country, And from the hill-country, And from the south, Bringing in burnt-offering, and sacrifice, And present, and frankincense, And bringing praise [to] the house of YHWH.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
And if you do not listen to Me to sanctify the day of rest, And so as not to bear a burden, And to come in at the gates of Jerusalem on the day of rest, Then I have kindled a fire in its gates, And it has consumed the high places of Jerusalem, And it is not quenched!”

< Irmiya 17 >