< Irmiya 17 >
1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
The sin of Judah is written down with a pen of iron, with the point of a diamond: it is engraved upon the table of their heart, and on the horns of your altars.
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
Like their remembrance of their children, so are [to them] their altars and their groves by [every] green tree upon the high hills.
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
O my mountain in the field, thy substance, all thy treasures will I give up for spoil, thy high-places [reared] with sin, throughout all thy borders.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
And thou shalt be cast out, yea through thy own guilt, from thy heritage which I have given thee; and I will cause thee to serve thy enemies in a land which thou knowest not; for a fire have ye kindled in my anger, for ever shall it burn.
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
Thus hath said the Lord, Cursed is the man that trusteth in man, and placeth on flesh his dependence, while from the Lord his heart departeth.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
And he shall be like a lonely tree in the desert, which feeleth not when the good cometh; but abideth in the parched places in the wilderness, in a salty land which cannot be inhabited.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Blessed is the man that trusteth in the Lord, and the Lord will be his trust.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
And he shall be like a tree that is planted by the waters, and by a stream spreadeth out its roots, which feeleth not when heat cometh, but its leaf remaineth green; and in a year of drought it is undisturbed by care, and ceaseth not from yielding fruit.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
Deceitful is the heart above all things, and sick: who can know it?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
I the Lord search the heart, probe the reins: yea, to give unto every man according to his ways, according to the fruit of his deeds.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
As a cuckoo that sitteth on eggs which he hath not laid, so is he that get the riches, and not by right; in the midst of his days shall he leave them, and at his end shall be called wicked.
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
A throne of glory, exalted from the beginning, is the place of our sanctuary!
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
Hope of Israel, O Lord, all that forsake thee shall be made ashamed, and the backsliders among me shall be written down on the earth; because they have forsaken the fountain of living waters, the Lord.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Heal me, O Lord, and I shall be healed: save me, and I shall be saved; for my praise art thou.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Behold, they say unto me, Where is the word of the Lord? let it come now.
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
As for me, I have not hastened to be a shepherd to follow thee; and the woeful day have I not longed for; thou knowest it: what came out of my lips was known before thee.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Be not a terror unto me: thou art my protection on the day of evil.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Let those be made ashamed that persecute me, but let not me be made ashamed: let them be dismayed, but let me not be dismayed: bring upon them the day of evil, and strike them with a double breach.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Thus said the Lord unto me, Go and stand in the gate of the children of the people, whereby the kings of Judah usually enter, and by which they usually go out, and in all the gates of Jerusalem;
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
And say unto them, Hear ye the word of the Lord, ye kings of Judah, and all Judah, and all inhabitants of Jerusalem, that enter in by these gates.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
Thus hath said the Lord, Take heed for your souls, and bear no burden on the sabbath-day, nor bring it in through the gates of Jerusalem;
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
Nor shall you carry forth a burden out of your houses on the sabbath-day, and no manner of work shall ye do, but hallow ye the sabbath-day, as I have commanded your fathers;
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
But they hearkened not, and inclined not their ear; and they made their neck stiff, so as not to hearken, and not to receive instruction.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
And it shall come to pass, if ye will diligently hearken unto me, saith the Lord, so as to bring in no burden through the gates of this city on the sabbath-day, and to hallow the sabbath-day, so as to do no work thereon:
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
Then shall there enter through the gates of this city kings and princes sitting upon the throne of David, riding in chariots and on horses, they, and their princes, the men of Judah, and the inhabitants of Jerusalem; and this city shall be inhabited for ever.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
And there shall come from the cities of Judah, and from the environs of Jerusalem, and from the land of Benjamin, and from the lowlands, and from the mountain, and from the south, those that bring burnt-offerings, and sacrifices, and meat-offerings, and frankincense, and those that bring thanksgiving-offerings, unto the house of the Lord.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
But if ye will not hearken unto me to hallow the sabbath-day, and not to bear a burden, and to enter in at the gates of Jerusalem on the sabbath-day: then will I kindle a fire in its gates, and it shall devour the palaces of Jerusalem, and it shall not be quenched.