< Irmiya 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Och Herrans ord skedde till mig, och sade:
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
Du skall ingen hustru taga dig, eller föda några söner eller döttrar i desso rumme.
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
Ty så säger Herren om de söner och döttrar, som i detta rummet födde varda, och om mödrarna som dem föda, och om deras fäder som dem föda i desso lande:
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
De skola dö af krankheter, och hvarken begråtne eller begrafne varda; utan skola till träck varda på markene; dertill skola de ock genom svärd och hunger förgås, och deras kroppar skola foglom under himmelen och djurom på markene till spis varda.
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
Ty så säger Herren: Du skall icke gå till begängelse, och skall ej heller någorstäds gå till begråtning, eller medlidande öfver dem hafva; ty jag hafver tagit min frid ifrå desso folke, säger Herren, samt med mine nåd och barmhertighet;
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
Att både store och små skola dö i desso lande, och intet begrafne, eller begråtne varda; och ingen skall rifva sig, eller raka sitt hår öfver dem.
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
Och man skall ej heller utskifta bröd i den begråtning, till att hugsvala dem öfver liket; och ej heller gifva dem dricka af tröstebägarenom öfver fader och moder.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
Derföre skall du intet gå in uti något dryckohus, till att sitta när dem; eller till att äta, eller till att dricka.
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
Ty så säger Herren Zebaoth, Israels Gud: Si, jag skall borttaga af desso rummena för edor ögon, och medan I än lefven, fröjds och glädjes röst, brudgummes och bruds röst.
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
Och när du allt detta desso folkena sagt hafver, och de säga till dig: Hvi talar Herren öfver oss alla denna stora olyckona? Hvilken är den missgerning eller synd, der vi med emot Herran vår Gud syndat hafve?
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
Så skall du säga dem: Derföre att edra fäder, säger Herren, hafva öfvergifvit mig, och följt andra gudar, tjent dem, och tillbedit dem; men mig hafva de förlåtit, och intet hållit min lag;
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
Och I ännu värre gören, än edre fäder; ty si, hvar och en lefver efter sins ondas hjertas tycko, på, det han icke skall lyda mig.
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
Derföre skall jag drifva eder utu detta landet, in uti ett land der hvarken I eller edre fäder af veten; der skolen I tjena andra gudar, dag och natt; och der skall jag ingen nåde bevisa eder.
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
Derföre, si, den tiden kommer, säger Herren, att man intet mer skall säga: Så sant som Herren lefver, som Israels barn utur Egypti land fört hafver;
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
Utan, så sant som Herren lefver, som Israels barn fört hafver utu nordlanden, och utur all land, dit han dem utdrifvit hafver; ty jag skall låta dem igen komma uti det land, som jag deras fäder gifvit hafver.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
Si, jag skall utsända många fiskare, säger Herren, de skola fiska dem; och derefter skall jag utsända många jägare, de skola fånga dem på all berg, på alla högar, och i alla stenklyftor.
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
Ty min ögon se uppå alla deras vägar, att de icke skola kunna gömma sig för mig; och deras missgerning är för min ögon fördold.
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
Men tillförene skall jag dubbelt betala deras missgerning och synd; derföre, att de hafva orenat mitt land med deras afguderis lik, och gjort mitt land fullt med sin styggelse.
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
Herre, du äst min starkhet och kraft, och min tillflykt uti nödene. Hedningarna skola komma till dig af verldenes ändar, och säga: Våre fäder hafva haft falska och fåfänga gudar, som intet hjelpa kunna.
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
Huru kan en menniska göra dem till gudar, som inge gudar äro?
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
Derföre si, nu vill jag lära dem, och göra dem mina hand och mitt välde kunnigt, att de skola förnimma att jag heter Herren.

< Irmiya 16 >