< Irmiya 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
Tu ne prendras point de femme, et tu n’auras point de fils et de filles en ce lieu.
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
Parce que voici ce que dit le Seigneur sur les fils et les filles qui sont enfantés en ce lieu, et sur les mères qui les ont enfantés, et sur leurs pères de la souche desquels ils sont nés en cette terre:
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
De différentes morts de maladies ils mourront; ils ne seront pas pleures et ils ne seront pas ensevelis; comme un fumier, ils seront sur la face de la terre; par le glaive et par la famine ils seront consumés, et leur cadavre sera en pâture aux volatiles du ciel et aux bêtes de la terre.
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
Car voici ce que dit le Seigneur: N’entre point dans une maison de festin; et ne va pas pour pleurer, et ne les console point; parce que j’ai retiré ma paix à ce peuple, dit le Seigneur, ma miséricorde et mes bontés.
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
Et ils mourront, grands et petits, sur cette terre, et ils ne seront pas ensevelis, ni pleures, et on ne se fera pas d’incision, et on ne se rasera pas la tête pour eux.
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
Et on ne rompra pas parmi eux de pain pour consoler celui qui pleure un mort, et on ne leur donnera pas le calice à boire pour le consoler de la perte de son père et de sa mère.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
Et tu n’entreras pas dans une maison d’un festin, afin de l’asseoir et de manger et de boire;
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Voilà que moi j’ôterai de ce lieu, à vos yeux et en vos jours, la voix de la joie et la voix de l’allégresse, la voix de l’époux et la voix de l’épouse.
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
Et lorsque tu annonceras à ce peuple toutes ces paroles, et qu’ils le diront: Pourquoi le Seigneur a-t-il prononcé sur nous tous ces grands maux? quelle est notre iniquité? et quel péché avons-nous commis contre le Seigneur notre Dieu?
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
Tu leur diras: C’est parce que vos pères m’ont abandonné, dit le Seigneur, qu’ils ont couru après des dieux étrangers, qu’ils les ont servis, qu’ils les ont adorés; et qu’ils m’ont abandonné, et qu’ils n’ont point gardé ma loi.
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
Mais vous-même, vous avez fait pis que vos pères; car voilà que chacun marche à la suite de la dépravation de son cœur mauvais, afin de ne pas m’écouter.
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
Et je vous jetterai de cette terre dans une terre que vous ignorez comme vos pères; et vous servirez là des dieux étrangers, le jour et la nuit, qui ne vous donneront pas de repos.
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
À cause de cela, voilà que des jours viennent, dit le Seigneur, et l’on ne dira plus: Le Seigneur vit! qui a retiré les fils d’Israël de la terre d’Egypte,
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
Mais: Vive le Seigneur qui a tiré les fils d’Israël de la terre de l’aquilon, et de toutes les terres où je les ai jetés; et je les ramènerai dans leur terre que j’ai donnée à leurs pères.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
Voilà que moi j’enverrai des pêcheurs nombreux, dit le Seigneur, et ils pécheront; et après cela je leur enverrai beaucoup de chasseurs, qui leur feront la chasse sur toute montagne, sur toute colline et dans toutes les cavernes des rochers;
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
Parce que mes yeux sont sur toutes les voies; elles ne sont pas cachées à ma face, et leur iniquité n’est pas voilée à mes yeux.
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
Et je leur rendrai d’abord au double leurs iniquités et leurs péchés, parce qu’ils ont souillé ma terre de morts pour leurs idoles, et que de leurs abominations ils ont rempli mon héritage.
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
Seigneur, mon courage, ma force et mon refuge au jour de la tribulation, vers vous viendront des nations des extrémités de la terre, et elles diront: Il est vrai que nos pères ont possédé le mensonge et la vanité, qui ne leur a pas été utile.
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
Est-ce qu’un homme se fera des dieux, lesquels même ne sont pas des dieux?
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
C’est pourquoi voici que moi je leur montrerai cette fois, je leur montrerai ma main et ma force, et ils sauront que mon nom est le Seigneur.

< Irmiya 16 >