< Irmiya 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
Tu ne te prendras point de femme et tu n’auras point de fils ni de filles en ce lieu-ci.
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
Car ainsi dit l’Éternel touchant les fils et les filles qui naissent en ce lieu, et touchant leurs mères qui les enfantent, et touchant les pères qui les engendrent dans ce pays:
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
Ils mourront de morts misérables; ils ne seront pas pleurés, et ne seront pas enterrés; ils seront du fumier sur la face du sol, et ils seront consumés par l’épée et par la famine, et leurs cadavres seront en pâture aux oiseaux des cieux et aux bêtes de la terre.
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
Car ainsi dit l’Éternel: N’entre pas dans la maison de lamentation, et ne va pas pour pleurer, et ne mène pas deuil sur eux; car j’ai ôté à ce peuple, dit l’Éternel, ma paix, – la bonté, et les compassions.
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
Et grands et petits mourront dans ce pays; ils ne seront pas enterrés, et on ne les pleurera point, et on ne se fera pas d’incision, ni ne se rendra chauve à cause d’eux.
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
Et on ne rompra pas pour eux le pain dans le deuil, en consolation au sujet d’un mort, et on ne leur donnera pas à boire la coupe des consolations pour leur père ou pour leur mère.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
Et tu n’entreras pas dans une maison de festin afin de t’asseoir avec eux pour manger et pour boire.
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
Car ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Voici, je vais faire cesser dans ce lieu-ci, devant vos yeux et en vos jours, la voix de l’allégresse et la voix de la joie, la voix de l’époux et la voix de l’épouse.
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
Et il arrivera que, quand tu annonceras à ce peuple toutes ces paroles, et qu’ils te diront: Pourquoi l’Éternel dit-il contre nous tout ce grand mal, et quelle est notre iniquité, et quel est notre péché que nous avons commis contre l’Éternel, notre Dieu?
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
alors tu leur diras: C’est parce que vos pères m’ont abandonné, dit l’Éternel, et sont allés après d’autres dieux, et les ont servis, et se sont prosternés devant eux, et m’ont abandonné, et n’ont point gardé ma loi;
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
et vous, vous avez fait pis encore que vos pères, et vous voilà marchant chacun suivant le penchant obstiné de son mauvais cœur, pour ne pas m’écouter;
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
et je vous jetterai de ce pays dans un pays que vous n’avez pas connu, ni vous, ni vos pères; et vous servirez là d’autres dieux, jour et nuit, parce que je ne vous témoignerai aucune faveur.
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
C’est pourquoi, voici, des jours viennent, dit l’Éternel, où on ne dira plus: L’Éternel est vivant, qui a fait monter les fils d’Israël du pays d’Égypte;
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
mais: L’Éternel est vivant, qui a fait monter les fils d’Israël du pays du nord, et de tous les pays où il les avait chassés. Et je les ramènerai dans leur terre, que j’ai donnée à leurs pères.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
Voici, je fais venir beaucoup de pêcheurs, dit l’Éternel, et ils les pêcheront; et après cela je ferai venir beaucoup de chasseurs, qui les prendront comme du gibier de dessus toutes les montagnes, et de dessus toutes les collines, et des trous des rochers.
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
Car mes yeux sont sur toutes leurs voies; elles ne sont pas cachées de devant ma face, ni leur iniquité mise à couvert de devant mes yeux.
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
Et je rendrai premièrement le double de leur iniquité et de leur péché, parce qu’ils ont souillé mon pays par les cadavres de leurs choses exécrables; et ils ont rempli mon héritage de leurs abominations.
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
Éternel, ma force, et ma forteresse, et mon refuge au jour de la détresse! à toi les nations viendront des bouts de la terre, et elles diront: Certainement nos pères ont hérité le mensonge, la vanité; et dans ces choses il n’y a point de profit.
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
L’homme se fera-t-il bien des dieux, qui ne sont pas des dieux?
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
C’est pourquoi, voici, cette fois je leur fais connaître, je leur ferai connaître ma main et ma puissance, et ils sauront que mon nom est l’Éternel.

< Irmiya 16 >