< Irmiya 16 >
1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Yahweh gave me another message. [He said to me],
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
“Do not get married and have children in this land,
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
because this is what [I], Yahweh, say about the children who are born in this city, and about their mothers and fathers:
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
[Many of] them will die from terrible diseases. And no one will mourn for them. No one will even bury their corpses; the corpses will lie on the ground, [scattered] like manure. [Others] will die in wars or from hunger, and [then] their corpses will become food for vultures and wild animals.”
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
This is [also] what Yahweh said to me: “Do not go to funerals to mourn or to show [those whose relatives have died] that you feel sorry for them, because I have stopped protecting them, and I have caused that things will not go well for them. I have stopped faithfully loving them and acting mercifully toward them.
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
[Very many people] will die in this land, [including] those who are important and those who are not important. And no one will mourn for them, or [even] bury [their corpses]. No one will cut himself or shave his head [to show that he is very sad].
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
No one will bring food to comfort those who are mourning, not even if it is their father or their mother [who has died]. No one will give them a cup [of wine] to cheer them up.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
And do not go into the houses where people are feasting. Do not eat or drink anything with them.
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
[I want you to do this] because this is what [I], the Commander of the armies of angels, say: ‘While you are still alive and seeing it happen, I will cause there to be no more singing and laughing in this land. There will be no more joyful voices of bridegrooms and brides.’
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
When you tell these things to the people, they will ask, ‘Why has Yahweh declared that these terrible things will happen to us? What have we done [for which we deserve to be punished like this]? What sin have we committed against Yahweh our God?’
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
Then this is what you must tell them [that I am replying to them]: ‘It is because your ancestors turned away from me, Yahweh. They worshiped other gods and served them. They abandoned me and did not obey my commands.
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
But you [who are living now] have done more wicked things than your ancestors did! Each of you stubbornly does the evil things that he desires and refuses to pay attention to what I say.
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
So, I will throw you out of this land, and I will send you to a land that you and your ancestors have never known about. There you will worship other gods day and night. And I will not act mercifully toward you.’
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
But there will be a time when people [who are solemnly promising to do something] will no longer say, ‘[I will do this], [just as surely] as Yahweh lives—the one who brought the Israeli people here from Egypt.’
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
Instead, they will say ‘[I will do this, just as surely] as Yahweh lives—the one who brought [us] Israeli people back to our own land, from the lands to the north and from all the other lands to which he had (exiled us/forced us to go).’ [They will be able to say that] because [some day] I will bring your descendants back to this land that I gave to your ancestors.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
But now I am summoning [your enemies who will seize the people of Judah like] [MET] fishermen [catch fish]. I am summoning those who will search for them on every mountain and hill, and in every cave, [like] [MET] hunters [search for animals to kill].
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
I am watching them carefully. I see every sin [that they commit]. They will not [be able to] hide from me [MTY].
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
Because of all the wicked things that they have done [DOU], I will punish them twice as much [as I would punish other people. I will do that] because they have caused my land to become unacceptable to me because of their [worshiping] lifeless statues of detestable gods, and [also because they] have done many other evil things throughout my land.”
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
[Then I prayed, saying], “Yahweh, you are the one who strengthens me and protects me [MET]; you are the one to whom I go when I have [troubles]. [Some day people from] nations all over the world will come to you and say, ‘Our ancestors left/gave us only something that was false; [they worshiped idols] that are completely worthless [DOU].
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
No one can [RHQ] make their own gods; the gods that they make are [only idols]; they are not real gods.’”
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
[Then Yahweh said], “Now I will show my power to [the people of Judah]; I will show them that I am truly very powerful [DOU]. Then, finally, they will know that I, Yahweh, [am the true God].”