< Irmiya 15 >
1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
Potem mi je Gospod rekel: »Čeprav bi pred menoj stala Mojzes in Samuel, vendar moj um ne bi mogel biti k temu ljudstvu. Vrzi jih iz mojega pogleda in naj gredo naprej.
2 In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
Zgodilo se bo, če ti rečejo: ›Kam naj gremo naprej?‹ Potem jim boš rekel: ›Tako govori Gospod: ›Tisti, ki ste za smrt, k smrti; tisti, ki ste za meč, k meču; tisti, ki ste za lakoto, k lakoti in tisti, ki ste za ujetništvo, k ujetništvu.‹
3 “Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
Nad njimi bom določil štiri vrste, ‹ govori Gospod: ›meč, da ubija in pse, da trgajo ter perjad neba in zemeljske živali, da požirajo in uničujejo.
4 Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
Povzročil jim bom, da bodo odstranjeni v vsa kraljestva zemlje, zaradi Manáseja, sina Ezekíja, Judovega kralja, za to, kar je storil v Jeruzalemu.
5 “Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
Kajti kdo bo imel usmiljenje nad teboj, oh [prestolnica] Jeruzalem? Kdo te bo obžaloval? Kdo bo šel vstran, da te vpraša, kako si?
6 Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
Zapustila si me, ‹ govori Gospod, ›umaknila si se nazaj. Zato bom zoper tebe iztegnil svojo roko in te uničil; izmučen sem od kesanja.
7 Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
Vejál jih bom z vejálnikom v velikih vratih dežele; oropal jih bom otrok, uničil bom svoje ljudstvo, ker se niso vrnili iz svojih poti.
8 Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
Njihove vdove so mi [številčno] narasle nad peskom morja. Zoper mater mladeničev sem nadnje opoldan privedel plenitelja. Storil sem mu, da je nenadoma padel nanjo in strahote so padle nad mesto.
9 Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
Tista, ki jih je rodila sedem, peša. Izročila je duha. Njeno sonce je zašlo, medtem ko je bil še dan. Bila je osramočena in zmedena. Preostanek izmed njih bom izročil meču pred njihovimi sovražniki, ‹« govori Gospod.
10 Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
»Gorje meni, moja mati, da si me rodila, človeka prepira in človeka spora celotni zemlji! Niti nisem posojal za obresti niti mi ljudje niso posojali za obresti, vendar me vsakdo izmed njih preklinja.«
11 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
Gospod je rekel: »Resnično, dobro bo s tvojim preostankom. Resnično, povzročil bom, da bo sovražnik dobro ravnal s teboj v času zla in v času stiske.
12 “Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
Se bo železo zlomilo, severno železo in jeklo?
13 “Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
Tvoje imetje in tvoje zaklade bom izročil v plen brez cene in to za vse tvoje grehe, celo v vseh tvojih mejah.
14 Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
Storil ti bom, da v deželo, ki je ne poznaš, preideš s svojimi sovražniki. Kajti ogenj je vnet v moji jezi, ki bo gorel na vas.«
15 Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
Oh Gospod, ti veš. Spomni se me in me obišči in me maščuj nad mojimi preganjalci. V svoji potrpežljivosti me ne odvzemi proč. Vedi, da sem zaradi tebe trpel grajo.
16 Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Tvoje besede so bile najdene in sem jih jedel, in tvoja beseda mi je bila radost in veselje mojega srca, kajti imenovan sem po tvojem imenu, oh Gospod, Bog nad bojevniki.
17 Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
Nisem sedel v zboru zasmehovalcev niti se nisem razveseljeval; sam sem sedel zaradi tvoje roke, kajti napolnil si me z ogorčenjem.
18 Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
Zakaj je moja bolečina neprestana in moja rana, ki odklanja biti ozdravljena, nezaceljiva? Ali mi hočete biti vsi skupaj kakor lažnivec in kakor vode, ki odpovedo?
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
Zato tako govori Gospod: »Če se spreobrneš, potem te bom ponovno privedel in boš stal pred menoj. Če odvzameš dragoceno iz hudobnega, boš kakor moja usta. Oni naj se vrnejo k tebi, toda ti se ne vrni k njim.
20 Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
Temu ljudstvu te bom naredil za ograjen bronast zid. Borili se bodo zoper tebe, toda ne bodo prevladali zoper tebe, kajti jaz sem s teboj, da te rešim in da te osvobodim, ‹ govori Gospod.
21 “Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”
›Rešil te bom iz roke zlobnih in odkupil te bom iz roke strašnih.‹«