< Irmiya 15 >

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
Et le Seigneur médit: Quand même Moïse et Samuel se présenteraient devant moi, mon âme ne serait pas pour ce peuple; chasse-les de ma face, et qu’ils se retirent.
2 In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
Que s’ils te disent: Où irons-nous? tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur: À la mort, ceux qui sont destinés à la mort; au glaive, ceux qui sont destinés au glaive; à la famine, ceux qui sont destinés à la famine; à la captivité, ceux qui sont destinés à la captivité.
3 “Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
Et je préposerai sur eux quatre espèces de fléaux, dit le Seigneur: le glaive pour tuer, les chiens pour déchirer, les oiseaux du ciel et les bêtes de la terre pour dévorer et pour mettre en pièces;
4 Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
Et je les livrerai comme objet de persécution à tous les royaumes de la terre, à cause de Manassé, fils d’Ezéchias, roi de Juda, pour tout ce qu’il a fait dans Jérusalem.
5 “Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
Car qui aura pitié de toi, Jérusalem? ou qui s’attristera pour toi? ou qui ira prier pour ta paix?
6 Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
Tu m’as abandonné, dit le Seigneur, tu es retournée en arrière; et j’étendrai ma main sur toi, et je te tuerai, je suis las de te prier.
7 Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
Et je les disperserai avec un van aux portes de la terre; j’ai tué, j’ai perdu entièrement mon peuple, et cependant ils ne sont pas revenus de leurs voies.
8 Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
Les veuves ont été multipliées par moi plus que le sable de la mer; j’ai amené parmi eux contre la mère du jeune homme un dévastateur en plein midi; j’ai envoyé soudainement sur les cités la terreur.
9 Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
Elle est devenue impuissante, celle qui avait enfanté sept fois; son âme a défailli; le soleil s’est couché pour elle, lorsqu’il était encore jour; elle a été confondue, et elle a rougi; et ceux qui restent de ses enfants, je les livrerai au glaive, en présence de leurs ennemis, dit le Seigneur.
10 Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
Malheur à moi, ma mère! pourquoi m’avez-vous enfanté homme de querelle, homme de discorde sur toute la terre? Je n’ai pas prêté à usure, et personne ne m’a prêté à intérêt; et cependant tous me maudissent.
11 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
Le Seigneur dit: Si tes débris n’arrivent pas au bonheur, si je ne vais pas au devant de toi au temps de la tribulation contre ton ennemi,
12 “Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
Est-ce que le fer s’alliera avec le fer qui vient de l’aquilon, et l’airain avec l’airain de l’aquilon?
13 “Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
Tes richesses et tes trésors, je les abandonnerai au pillage sans aucun profit, à cause de tous tes péchés, et cela dans tous les confins.
14 Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
Et j’amènerai tes ennemis d’une terre que tu ne connais pas, parce qu’un feu s’est allumé dans ma fureur et qu’il vous embrasera.
15 Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
Vous savez mon affliction. Seigneur, souvenez-vous de moi, venez vers moi et protégez-moi contre ceux qui me persécutent; et ne soyez pas lent à me défendre; sachez que c’est pour vous que je supporte l’opprobre.
16 Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Vos discours me sont parvenus, et je les ai dévorés, et votre parole est devenue la joie et le ravissement de mon cœur; parce que votre nom a été invoqué sur moi, Seigneur Dieu des armées.
17 Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
Je ne me suis pas assis dans l’assemblée des railleurs; je me suis glorifié à cause de votre main; j’étais assis seul, parce que vous m’avez rempli de vos menaces.
18 Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
Pourquoi ma douleur est-elle devenue continuelle, et pourquoi ma plaie désespérée refuse-t-elle de se guérir? elle est devenue pour moi comme le mensonge des eaux infidèles.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Si tu te convertis, je te convertirai, et tu te tiendras devant ma face, et si tu sépares ce qui est précieux de ce qui est vil, tu seras comme ma bouche; ils se tourneront eux vers toi; mais tu ne te retourneras pas vers eux.
20 Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
Et je te donnerai à ce peuple comme un mur d’airain solide; et ils combattront contre toi, mais ils ne prévaudront pas, parce que moi je suis avec toi pour te sauver et te délivrer, dit le Seigneur.
21 “Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”
Et je te délivrerai de la main des méchants, et je t’arracherai à la main des forts.

< Irmiya 15 >