< Irmiya 15 >

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da Musa da Sama’ila za su tsaya a gabana, zuciyata ba za tă komo ga mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana! Su tafi!
Et l'Eternel me dit: quand Moïse et Samuel se tiendraient devant moi, je n'aurais pourtant point d'affection pour ce peuple; chasse-les de devant ma face, et qu'ils sortent.
2 In kuma suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Waɗanda aka ƙaddara ga mutuwa, ga mutuwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga takobi, ga takobi za su; waɗanda aka ƙaddara ga yunwa, ga yunwa za su; waɗanda aka ƙaddara ga zaman bauta, ga zaman bauta za su.’
Que s'ils te disent: où sortirons-nous? Tu leur répondras: ainsi a dit l'Eternel: ceux qui [sont destinés] à la mort [iront] à la mort; et ceux qui [sont destinés] à l’épée [iront] à l’épée; et ceux qui [sont destinés] à la famine, [iront] à la famine; et ceux qui [sont destinés] à la captivité [iront] en captivité.
3 “Zan aika musu da iri masu hallakarwa guda huɗu,” in ji Ubangiji, “takobi zai kashe, karnuka za su kwashe, tsuntsaye da namun jeji kuma su cinye su kuma hallaka.
J'établirai aussi sur eux quatre espèces de [punitions], dit l'Eternel, l'épée pour tuer, et les chiens pour traîner, et les oiseaux des cieux, et les bêtes de la terre pour dévorer et pour détruire.
4 Zan sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manasse ɗan Hezekiya sarkin Yahuda ya aikata a Urushalima.
Et je les livrerai à être agités par tous les Royaumes de la terre, à cause de Manassé fils d'Ezéchias, Roi de Juda, pour les choses qu'il a faites dans Jérusalem.
5 “Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi makoki dominki? Wa zai dakata ya tambayi lafiyarki?
Car qui serait ému de compassion envers toi, Jérusalem? ou qui viendrait se condouloir avec toi? ou qui se détournerait pour s'enquérir de ta prospérité?
6 Kin ƙi ni,” in ji Ubangiji. “Ki ci gaba da ja da baya. Ta haka zan ɗibiya hannuwana a kanki in hallaka ki; ba zan ƙara nuna miki jinƙai ba.
Tu m'as abandonné, dit l'Eternel, et tu t'en es allée en arrière; c'est pourquoi j'étendrai ma main sur toi, et je te détruirai; je suis las de me repentir.
7 Zan sheƙe ki da abin sheƙewa a ƙofofin birnin ƙasar. Zan kawo baƙin ciki da hallaka a kan mutanena, gama ba su canja hanyoyinsu ba.
Je les vannerai avec un van aux portes du pays; j'ai désolé [et] fait périr mon peuple, et ils ne se sont point détournés de leur voie.
8 Zan ƙara yawan gwaurayensu su fi yashin teku yawa. Da tsakar rana zan kawo mai hallakarwa a kan iyaye mata na samarinsu; farat ɗaya zan kawo musu wahala da razana.
J'ai multiplié ses veuves plus que le sable de la mer, je leur ai amené sur la mère de leur jeunesse un destructeur en plein midi, j'ai fait tomber subitement sur elle l'ennemi et les frayeurs.
9 Mahaifiya’ya’ya bakwai za tă suma ta ja numfashinta na ƙarshe. Ranarta zai fāɗi tun lokacin bai yi ba; za tă sha kunya a kuma wulaƙanta ta. Zan sa a kashe raguwa da takobi a gaban abokan gābansu,” in ji Ubangiji.
Celle qui en avait enfanté sept est devenue languissante, elle a rendu l'esprit, son soleil lui est couché pendant qu'il était encore jour, elle a été rendue honteuse et confuse; et je livrerai son reste à l'épée devant leurs ennemis, dit l'Eternel.
10 Kaitona, mahaifiyata, da kika haife ni, mutumin da dukan ƙasa take faɗa take kuma gardama da shi! Ban ba da bashi ko in ci bashi ba, duk da haka kowa yana zagina.
Malheur à moi, ô ma mère! de ce que tu m'as enfanté pour être un homme de débat, et un homme de querelle à tout le pays; je ne me suis obligé à personne, et personne ne s'est obligé à moi, et néanmoins chacun me maudit et me méprise.
11 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce zan cece ka don alheri; tabbatacce zan sa abokan gābanka su yi roƙo gare ka a lokacin masifa da kuma lokacin wahala.
[Alors l'Eternel dit: ] ceux qui seront restés de toi ne viendront-ils pas à bien? et ne ferai-je pas que l'ennemi viendra au devant de toi au temps de la calamité, et au temps de la détresse?
12 “Mutum zai iya karye ƙarfe ƙarfe daga arewa, ko tagulla?
Le fer usera-t-il le fer de l'Aquilon, et l'acier?
13 “Dukiyarku da arzikinku zan ba da su ganima, babu tara, saboda duka zunubanku ko’ina a ƙasar.
Je livrerai au pillage, sans en faire le prix, tes richesses et tes trésors; et cela à cause de tous tes péchés, et même par toutes tes contrées.
14 Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina zai yi ƙuna kamar wuta da za tă yi ƙuna a kanku.”
Et je ferai passer tes ennemis par un pays que tu ne connais point, car le feu a été allumé en ma colère, il sera allumé sur vous.
15 Ka gane, ya Ubangiji; ka tuna da ni ka kuma lura da ni. Ka yi mini ramuwa a kan masu tsananta mini. Cikin jimirinka, kada ka ɗauke ni; ka tuna yadda na sha zagi saboda kai.
Eternel, tu le connais, souviens-toi de moi, et me visite, et me venge de ceux qui me persécutent; ne m'enlève point, quand tu auras longtemps différé ta colère; connais que j'ai souffert opprobre pour l'amour de toi.
16 Sa’ad da maganganunka suka zo, na cinye su; suka zama abin farin ciki zuciyata kuma ta yi murna, gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Tes paroles se sont-elles trouvées? je les ai [aussitôt] mangées; et ta parole m'a été en joie, et elle a été l'allégresse de mon cœur; car ton Nom est réclamé sur moi, ô Eternel! Dieu des armées.
17 Ban taɓa zauna a cikin’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
Je ne me suis point assis au conventicule des railleurs, et je ne m'y suis point réjoui; mais je me suis tenu assis tout seul, à cause de ta main, parce que tu m'as rempli d'indignation.
18 Me ya sa wahalata ba ta ƙarewa mikina kuma ba ya warkuwa? Za ka zama mini kamar rafi mai yaudara ne, kamar maɓulɓulan da ta kafe ne?
Pourquoi ma douleur est-elle [rendue] continuelle, et ma plaie est-elle sans espérance? elle a refusé d'être guérie; me serais-tu bien comme une chose qui trompe? [comme] des eaux qui ne durent pas?
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “In ka tuba, zan maido da kai don ka bauta mini; in ka ambaci maganganu masu kyau, ba marasa kyau ba, za ka zama kakakina. Bari wannan mutane su juyo gare ka, amma kada ka juye gare su.
C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel: si tu te retournes, je te ramènerai, et tu te tiendras devant moi; et si tu sépares la chose précieuse de la méprisable, tu seras comme ma bouche; qu'ils se retournent vers toi, mais toi ne retourne pas vers eux.
20 Zan mai da kai katanga ga wannan mutane, katanga mai ƙarfi na tagulla; za su yi yaƙi da kai amma ba za su yi nasara a kanka ba, gama ina tare da kai don in kuɓutar in kuma cece ka,” in ji Ubangiji.
Et je te ferai être à l'égard de ce peuple une muraille d'acier bien forte; ils combattront contre toi, mais ils n'auront point le dessus contre toi, car je [suis] avec toi pour te garantir, et pour te délivrer, dit l'Eternel.
21 “Zan cece ka daga hannuwan mugaye in ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”
Et je te délivrerai de la main des malins, et te rachèterai de la main des terribles.

< Irmiya 15 >