< Irmiya 13 >

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
Så sa Herren til mig: Gå og kjøp dig et lerretsbelte og legg det om dine lender, men la det ikke komme i vann!
2 Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
Og jeg kjøpte beltet efter Herrens ord og la det om mine lender.
3 Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
Og Herrens ord kom til mig annen gang, og det lød så:
4 “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
Ta det belte du kjøpte, det som er om dine lender, og stå op, gå til Eufrat og skjul det der i en bergkløft!
5 Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
Og jeg gikk og skjulte det ved Eufrat, som Herren hadde befalt mig.
6 Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
Og lang tid efter sa Herren til mig: Stå op, gå til Eufrat og hent derfra det belte som jeg bød dig å skjule der.
7 Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
Og jeg gikk til Eufrat og gravde og tok beltet fra det sted hvor jeg hadde skjult det; og se, beltet var ødelagt, det dudde ikke til noget.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Da kom Herrens ord til mig:
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
Så sier Herren: Således vil jeg gjøre ende på Judas og Jerusalems store overmot.
10 Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
Dette onde folk, som ikke vil høre på mine ord, som følger sitt hårde hjerte og går efter andre guder for å dyrke og tilbede dem, det skal bli lik dette belte som ikke duer til noget!
11 Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
For likesom beltet fester sig til en manns lender, således festet jeg hele Israels hus og hele Judas hus til mig, sier Herren, forat det skulde være mitt folk og være mig til navnkundighet og til pris og til pryd; men de hørte ikke.
12 “Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
Og du skal si til dem dette ord: Så sier Herren, Israels Gud: Hver vinkrukke blir fylt med vin. Og de skal si til dig: Vet vi da ikke at hver vinkrukke blir fylt med vin?
13 Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
Og da skal du si til dem: Så sier Herren: Se, jeg fyller alle dette lands innbyggere og kongene som sitter på Davids trone, og prestene og profetene og alle Jerusalems innbyggere, så de blir drukne.
14 Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
Og jeg vil knuse dem, den ene mot den andre, både fedrene og barna alle sammen, sier Herren; jeg vil ikke skåne og ikke spare og ikke forbarme mig, så jeg lar være å ødelegge dem.
15 Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
Hør og gi akt, vær ikke overmodige! For Herren taler.
16 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
Gi Herren eders Gud ære, før han lar det bli mørkt, og før eders føtter støter sig på de mørke fjell! I venter på lys, og han gjør det til dødsskygge, lar det bli til belgmørke!
17 Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
Men vil I ikke høre på dette, da skal min sjel gråte i lønndom over slikt overmot, og mitt øie skal gråte så tårene triller, fordi Herrens hjord blir bortført i fangenskap.
18 Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
Si til kongen og til kongens mor: Sett eder ned i det lave! For eders prektige krone er falt av eders hode.
19 Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
Sydlandets byer er lukket, og det er ingen som lukker op; hele Juda er bortført, det er bortført, til siste mann.
20 Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
Løft eders øine og se dem som kommer fra Norden! Hvor er nu den hjord som var gitt dig, dine herlige får?
21 Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
Hvad vil du si når han setter fortrolige venner til høvdinger over dig, dem som du selv har oplært til det? Skulde ikke veer gripe dig, som en fødende kvinne?
22 In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
Og når du sier i ditt hjerte: Hvorfor har dette hendt mig? så vit: For dine mange misgjerningers skyld er kanten på din kjole løftet op, dine hæler blottet med vold.
23 Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
Kan en morian omskifte sin hud, eller en leopard sine flekker? - Da kan også I gjøre godt, I som er vant til å gjøre ondt.
24 “Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
Så vil jeg da adsprede dem likesom strå som farer avsted for ørkenens vind.
25 Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
Dette er din lodd, din tilmålte del fra mig, sier Herren, fordi du har glemt mig og satt din lit til løgn.
26 Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
Så vil da også jeg løfte kanten på din kjole op over ditt ansikt, så din skam blir sett.
27 zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
Ditt horelevnet og din vrinsken, din skammelige utukt på haugene ute på marken, ja dine vederstyggeligheter har jeg sett. Ve dig, Jerusalem! Hvor lenge vil det ikke ennu vare før du blir ren!

< Irmiya 13 >