< Irmiya 13 >

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
TUHAN menyuruh aku pergi membeli sarung pendek dari lenan dan memakainya, tapi aku tidak boleh mencelupkannya ke dalam air.
2 Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
Maka pergilah aku membeli sarung pendek itu, lalu memakainya.
3 Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
Kemudian TUHAN berbicara lagi kepadaku, katanya,
4 “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
"Pergilah ke Sungai Efrat, dan sembunyikan sarung pendek itu di celah-celah batu."
5 Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
Maka sesuai dengan perintah TUHAN pergilah aku dan menyembunyikan sarung pendek itu di dekat Sungai Efrat.
6 Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
Beberapa waktu kemudian TUHAN menyuruh aku pergi lagi ke Sungai Efrat untuk mengambil sarung pendek itu.
7 Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
Maka pergilah aku, dan mengeluarkan sarung pendek itu dari tempat aku menyembunyikannya. Ternyata sarung itu sudah lapuk, dan sama sekali tidak berguna lagi.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Lalu TUHAN berbicara lagi kepadaku, kata-Nya,
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
"Begitulah caranya Aku akan bertindak terhadap orang Yehuda dan penduduk Yerusalem. Aku akan menghancurkan keangkuhan mereka yang luar biasa itu.
10 Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
Bangsa yang jahat ini sangat keras kepala dan tak mau taat kepada-Ku. Mereka beribadat dan berbakti kepada ilah-ilah lain. Itu sebabnya mereka akan menjadi seperti sarung pendek yang tak berguna itu.
11 Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
Seperti sarung pendek terikat erat pada pinggang pemakainya, demikianlah Aku bermaksud supaya umat Israel dan Yehuda terikat erat pada-Ku. Dengan demikian mereka menjadi umat-Ku yang membuat nama-Ku terpuji dan dihormati. Tapi, mereka tidak mau menurut kepada-Ku."
12 “Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
TUHAN Allah berkata kepadaku, "Yeremia, sampaikanlah pesan-Ku kepada orang Israel bahwa setiap guci tempat anggur harus diisi penuh dengan anggur. Mereka akan menjawab, 'Masakan kami tidak tahu bahwa setiap guci harus dipenuhi dengan anggur?'
13 Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
Maka katakanlah kepada mereka bahwa orang-orang di negeri ini, raja-raja keturunan Daud, para imam, nabi, dan seluruh penduduk Yerusalem akan Kuisi penuh dengan anggur sampai mabuk.
14 Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
Lalu mereka akan Kubenturkan satu sama lain. Tua dan muda akan Kuperlakukan demikian tanpa ampun. Mereka akan Kubinasakan tanpa merasa sayang atau kasihan. Aku, TUHAN, telah berbicara."
15 Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
Umat Israel, TUHAN telah berbicara! Jangan angkuh, dengarkan Dia!
16 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
TUHAN Allahmu harus kauagungkan sebelum Ia mendatangkan kegelapan, dan kakimu tersandung di pegunungan, sebelum terang yang kauharapkan diubah-Nya menjadi kekelaman.
17 Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
Jika kau enggan mendengarkan, aku akan menangis dengan diam-diam. Dengan rasa pilu kutangisi keangkuhanmu itu. Air mataku akan berlinang karena umat TUHAN diangkut sebagai tawanan.
18 Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
TUHAN berkata kepadaku, "Suruh raja dan ibu suri turun dari takhtanya, sebab mahkotanya yang indah sudah jatuh dari kepalanya.
19 Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
Kota-kota Yehuda di bagian selatan sedang dikepung, dan tak ada yang dapat menerobosi kepungan itu. Semua orang Yehuda sudah diangkut ke pembuangan."
20 Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
TUHAN berkata kepada penduduk Yerusalem, "Perhatikanlah! Musuh-musuhmu sedang datang dari utara! Di manakah orang-orang yang harus kamu lindungi dan yang sangat kamu banggakan itu.
21 Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
Apa yang akan kamu katakan jika orang-orang yang kamu perlakukan sebagai kawan-kawanmu mengalahkan dan menguasai kamu? Pasti kamu akan merasa sakit seperti wanita yang sedang melahirkan.
22 In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
Barangkali kamu bertanya mengapa semuanya itu menimpa dirimu, mengapa pakaianmu dirobek dan kamu diperkosa. Ketahuilah bahwa itu terjadi karena dosamu terlalu besar.
23 Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
Dapatkah orang hitam mengubah warna kulitnya, atau harimau menghilangkan belangnya? Tentu tidak! Begitu juga kamu yang biasa berbuat jahat tidak mungkin berbuat baik.
24 “Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
Aku akan menceraiberaikan kamu seperti sekam ditiup angin dari padang gurun.
25 Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
Itulah nasibmu yang telah Kutentukan karena kamu telah melupakan Aku, dan telah percaya kepada ilah-ilah palsu.
26 Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
Aku sendiri akan merobek pakaian dari badanmu supaya kamu menjadi telanjang dan malu.
27 zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
Aku sudah melihat kamu melakukan hal-hal yang Kubenci. Aku telah melihat kamu mengejar ilah-ilah lain di bukit dan di ladang, seperti seorang laki-laki tergila-gila terhadap istri orang lain atau seperti kuda jantan bernafsu terhadap kuda betina. Penduduk Yerusalem, celakalah kamu! Kapan kamu akan bebas dari semua kejahatan?"

< Irmiya 13 >