< Irmiya 13 >

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
Ainsi m’a dit l’Éternel: Va, et achète-toi une ceinture de lin, et mets-la sur tes reins, et ne la trempe pas dans l’eau.
2 Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
Et j’achetai une ceinture, selon la parole de l’Éternel, et je la mis sur mes reins.
3 Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi pour la seconde fois, disant:
4 “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
Prends la ceinture que tu as achetée, qui est sur tes reins, et lève-toi, va vers l’Euphrate, et là, cache-la dans le creux d’un rocher.
5 Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
Et je m’en allai, et la cachai dans l’Euphrate, comme l’Éternel m’avait commandé.
6 Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
Et il arriva, à la fin de plusieurs jours, que l’Éternel me dit: Lève-toi, va vers l’Euphrate, et prends de là la ceinture que je t’avais commandé d’y cacher.
7 Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
Et je m’en allai vers l’Euphrate, et je creusai, et je pris la ceinture du lieu où je l’avais cachée; et voici, la ceinture était gâtée, elle n’était plus bonne à rien.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
Ainsi dit l’Éternel: C’est ainsi que je détruirai l’orgueil de Juda, et le grand orgueil de Jérusalem.
10 Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
Ce peuple mauvais, qui refuse d’écouter mes paroles, qui marche dans l’obstination de son cœur, et qui marche après d’autres dieux pour les servir et pour se prosterner devant eux, sera comme cette ceinture qui n’est bonne à rien.
11 Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
Car, comme une ceinture s’attache aux reins d’un homme, ainsi je me suis attaché toute la maison d’Israël et toute la maison de Juda, dit l’Éternel, pour être mon peuple, et un renom, et une louange, et un ornement; mais ils n’ont pas écouté.
12 “Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
Et tu leur diras cette parole: Ainsi dit l’Éternel, le Dieu d’Israël: Toute cruche sera remplie de vin. Et ils te diront: Ne savons-nous pas bien que toute cruche sera remplie de vin?
13 Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
Et tu leur diras: Ainsi dit l’Éternel: Voici, je remplis d’ivresse tous les habitants de ce pays, et les rois [issus] de David, qui sont assis sur son trône, et les sacrificateurs, et les prophètes, et tous les habitants de Jérusalem;
14 Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
et je les briserai l’un contre l’autre, et les pères et les fils ensemble, dit l’Éternel; je n’aurai pas de compassion, et je n’épargnerai pas, et je n’aurai pas de pitié pour ne pas les détruire.
15 Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
Écoutez, et prêtez l’oreille! Ne vous élevez point, car l’Éternel a parlé!
16 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
Donnez gloire à l’Éternel, votre Dieu, avant qu’il fasse venir des ténèbres, et avant que vos pieds se heurtent contre les montagnes du crépuscule: vous attendrez la lumière, et il en fera une ombre de mort et la réduira en obscurité profonde.
17 Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
Et si vous n’écoutez pas ceci, mon âme pleurera en secret à cause de votre orgueil, et mon œil pleurera amèrement et se fondra en larmes, car le troupeau de l’Éternel est allé en captivité.
18 Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
Parle au roi et à la reine: Humiliez-vous, asseyez-vous [par terre]; car la couronne de votre magnificence est descendue de dessus vos têtes.
19 Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
Les villes du midi sont fermées, et il n’y a personne qui les ouvre; tout Juda est transporté, il est tout entier transporté.
20 Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
Levez vos yeux, et voyez ceux qui viennent du nord. Où est le troupeau qui t’a été donné, le troupeau de ta gloire?
21 Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
Que diras-tu quand il te punira? Toi-même tu les as enseignés à être princes et chefs sur toi. Les douleurs ne te saisiront-elles pas comme une femme qui enfante?
22 In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
Et si tu dis en ton cœur: Pourquoi me sont arrivées ces choses? C’est par la multitude de tes iniquités que les pans de ta robe ont été découverts, [et] que tes talons ont été violemment déchaussés.
23 Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
L’Éthiopien peut-il changer sa peau, et le léopard ses taches? [Alors] aussi vous pourrez faire le bien, vous qui êtes instruits à faire le mal. –
24 “Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
Et je les disperserai comme le chaume qui s’en va par le vent du désert.
25 Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
C’est là ton lot, ta portion mesurée de par moi, dit l’Éternel, parce que tu m’as oublié, et que tu t’es confiée au mensonge.
26 Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
Et moi aussi, je relèverai tes pans sur ton visage, et ta honte se verra.
27 zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
Tes adultères, tes hennissements, l’infamie de ta prostitution sur les collines, dans les champs, – tes abominations, je [les] ai vues. Malheur à toi, Jérusalem! Ne te purifieras-tu pas, … après combien de temps encore?

< Irmiya 13 >