< Irmiya 13 >

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
Yahweh said this to me, “Go and buy a linen undergarment and put it on around your waist, but do not put it in water first.”
2 Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
So I bought an undergarment as Yahweh directed, and I put in on around my waist.
3 Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
Then the word of Yahweh came to me a second time, saying,
4 “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
“Take the undergarment that you purchased that is around your waist, get up and go now to Perath. Hide it there in a rock crevice.”
5 Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
So I went and hid it in Perath, just as Yahweh had commanded me.
6 Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
After many days, Yahweh said to me, “Get up and go back to Perath. Take from there the undergarment that I had told you to hide.”
7 Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
So I went back to Perath and dug out the undergarment where I had hid it, and behold, it was destroyed and completely useless.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
“Yahweh says this: In the same way I will destroy the great arrogance of Judah and Jerusalem.
10 Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
This wicked people who refuses to listen to my word, who walk in the hardness of their heart, who go after other gods to worship them and bow down to them—they will be like this undergarment that is good for nothing.
11 Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
For just as an undergarment clings to someone's hips, so I have made all the house of Israel and all the house of Judah cling to me—this is Yahweh's declaration—to be my people, to bring me fame, praise, and honor. But they would not listen to me.
12 “Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
So you must speak this word to them, 'Yahweh, the God of Israel, says this: Every jar will be filled with wine.' They will say to you, 'Do we not indeed know that every jar will be filled with wine?'
13 Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
So say to them, 'Yahweh says this: See, I am about to fill with drunkenness every inhabitant of this land, the kings who sit on David's throne, the priests, prophets, and all the inhabitants of Jerusalem.
14 Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
Then I will smash each man against the other, fathers and children together—this is Yahweh's declaration—I will not pity them or have compassion, and I will not spare them from destruction.'”
15 Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
Listen and pay attention. Do not be arrogant, for Yahweh had spoken.
16 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
Give honor to Yahweh your God before he brings darkness, and before he causes your feet to stumble on the mountains at twilight. For you are hoping for light, but he will turn the place into a deep darkness, into a dark cloud.
17 Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
So if you will not listen, I will weep alone because of your arrogance. My eyes will certainly weep and flow with tears, for Yahweh's flock has been taken captive.
18 Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
“Say to the king and to the queen mother, 'Come down from your thrones, for your splendid crowns have fallen from your heads.'
19 Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
The cities in the Negev will be shut up, with no one to open them. All Judah will be taken captive, completely taken captive.
20 Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
Lift up your eyes and look at the ones coming from the north. Where is the flock he gave to you, the flock that was so beautiful to you?
21 Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
What will you say when God sets over you those you had trained to be your special allies? Are these not the beginnings of the labor pains that will seize you just like a woman in childbirth?
22 In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
Then you might say in your heart, 'Why are these things happening to me?' It will be for the multitude of your iniquities that your skirts are raised up and you have been violated.
23 Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
Can the people of Cush change their skin color, or a leopard change its spots? If so, then you yourself, although accustomed to wickedness, would be able to do good.
24 “Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
So I will scatter them like chaff that perishes in the desert wind.
25 Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
This is what I have given to you, the portion I have decreed for you—this is Yahweh's declaration— because you have forgotten me and trusted in deceit.
26 Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
So also I myself will strip your skirts off you, and your private parts will be seen.
27 zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
I have seen your adultery and neighing, the wickedness of your prostitution on the hills and in the fields, and I have seen these detestable things! Woe to you, Jerusalem! How long until you are made clean again?”

< Irmiya 13 >