< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Você é justo, Yahweh, quando eu contendo com você; no entanto, eu gostaria de defender um caso com você. Por que o caminho dos ímpios prospera? Por que todos eles estão à vontade, que lidam de forma muito traiçoeira?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Você os plantou. Sim, eles criaram raízes. Elas crescem. Sim, eles produzem frutas. Você está por perto na boca deles, e longe de seu coração.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
Mas você, Yahweh, me conhece. Você me vê, e testa meu coração para você. Puxe-os para fora como ovelhas para o abate, e prepará-los para o dia do abate.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Quanto tempo a terra vai lamentar, e as ervas de todo o país murcham? Por causa da perversidade daqueles que habitam ali, os animais e as aves são consumidos; porque eles disseram, “Ele não verá nosso último fim”.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
“Se você já correu com os criados de libré, e eles o cansaram, então como você pode lutar com os cavalos? Embora em uma terra de paz você esteja seguro, no entanto, como você se sentirá no orgulho do Jordão?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
Até mesmo para seus irmãos, e para a casa de seu pai, mesmo eles lidaram traiçoeiramente com você! Mesmo eles choraram em voz alta depois de você! Não acredite neles, embora eles digam belas palavras para você.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
“Eu abandonei minha casa. Eu abandonei minha herança. Eu entreguei a amada de minha alma na mão de seus inimigos.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Minha herança se tornou para mim como um leão na floresta. Ela pronunciou sua voz contra mim. Portanto, eu a odiei.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Minha herança é para mim como ave de rapina salpicada? As aves de rapina estão contra ela por toda parte? Vá, monte todos os animais do campo. Traga-os para devorar.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Muitos pastores destruíram meu vinhedo. Eles pisaram minha porção sob os pés. Eles fizeram de minha agradável porção uma região desolada e selvagem.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
Eles fizeram disso uma desolação. Para mim é um pesar, estar desolado. Toda a terra se torna desolada, porque ninguém se importa.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Destruidores vieram em todas as alturas nus do deserto; para a espada de Iavé devora de uma ponta da terra até a outra ponta da terra. Nenhuma carne tem paz.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
Eles semearam trigo, e colheram espinhos. Eles se esgotaram, e não lucrar nada. Você terá vergonha de seus frutos, por causa da raiva feroz de Yahweh”.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Yahweh diz: “A respeito de todos os meus vizinhos maus, que tocam a herança que fiz herdar ao meu povo Israel: Eis que os arrancarei de suas terras, e arrancarei a casa de Judá do meio deles.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
Acontecerá que, depois de tê-los arrancado, voltarei e terei compaixão por eles. Eu os trarei novamente, cada homem à sua herança, e cada homem à sua terra.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
Acontecerá, se eles aprenderem diligentemente os caminhos do meu povo, jurando pelo meu nome, 'Como Javé vive'; mesmo que eles tenham ensinado meu povo a jurar por Baal, então eles serão construídos no meio do meu povo.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
Mas se eles não ouvirem, então eu arrancarei aquela nação, arrancando e destruindo-a”, diz Yahweh.

< Irmiya 12 >