< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
ای خداوند تو عادل تر هستی از اینکه من با تو محاجه نمایم. لیکن درباره احکامت با تو سخن خواهم راند. چرا راه شریران برخوردار می‌شود و جمیع خیانتکاران ایمن می‌باشند؟۱
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
تو ایشان را غرس نمودی پس ریشه زدند و نمو کرده، میوه نیز آوردند. تو به دهان ایشان نزدیکی، اما از قلب ایشان دور.۲
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
اما تو‌ای خداوند مرا می‌شناسی و مرا دیده، دل مرا نزدخود امتحان کرده‌ای. ایشان را مثل گوسفندان برای ذبح بیرون کش و ایشان را به جهت روز قتل تعیین نما.۳
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
زمین تا به کی ماتم خواهد نمود و گیاه تمامی صحرا خشک خواهد ماند. حیوانات ومرغان به‌سبب شرارت ساکنانش تلف شده اندزیرا می‌گویند که او آخرت ما را نخواهد دید.۴
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
اگر وقتی که با پیادگان دویدی تو را خسته کردند پس چگونه با اسبان می‌توانی برابری کنی؟ و هر‌چند در زمین سالم، ایمن هستی در طغیان اردن چه خواهی کرد؟۵
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
زیرا که هم برادرانت وهم خاندان پدرت به تو خیانت نمودند و ایشان نیزدر عقب تو صدای بلند می‌کنند پس اگر‌چه سخنان نیکو به تو بگویند ایشان را باور مکن.۶
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
من خانه خود را ترک کرده، میراث خویش رادور انداختم. و محبوبه خود را به‌دست دشمنانش تسلیم نمودم.۷
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
و میراث من مثل شیرجنگل برای من گردید. و به ضد من آواز خود رابلند کرد از این جهت از او نفرت کردم.۸
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
آیامیراث من برایم مثل مرغ شکاری رنگارنگ که مرغان دور او را گرفته باشند شده است؟ بروید وجمیع حیوانات صحرا را جمع کرده، آنها رابیاورید تا بخورند.۹
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
شبانان بسیار تاکستان مراخراب کرده، میراث مرا پایمال نمودند. و میراث مرغوب مرا به بیابان ویران مبدل ساختند.۱۰
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
آن را ویران ساختند و آن ویران شده نزد من ماتم گرفته است. تمامی زمین ویران شده، چونکه کسی این را در دل خود راه نمی دهد.۱۱
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
بر تمامی بلندیهای صحرا، تاراج کنندگان هجوم آوردندزیرا که شمشیر خداوند از کنار زمین تا کناردیگرش هلاک می‌کند و برای هیچ بشری ایمنی نیست.۱۲
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
گندم کاشتند و خار درویدند، خویشتن را به رنج آورده، نفع نبردند. و از محصول شما به‌سبب حدت خشم خداوند خجل گردیدند.۱۳
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
خداوند درباره جمیع همسایگان شریرخود که ضرر می‌رسانند به ملکی که قوم خوداسرائیل را مالک آن ساخته است چنین می‌گوید: «اینک ایشان را از آن زمین برمی کنم و خاندان یهودا را از میان ایشان برمی کنم.۱۴
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
و بعد ازبرکندن ایشان رجوع خواهم کرد و بر ایشان ترحم خواهم نمود و هر کس از ایشان را به ملک خویش و هر کس را به زمین خود باز خواهم آورد.۱۵
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
و اگر ایشان طریق های قوم مرا نیکو یادگرفته، به اسم من یعنی به حیات یهوه قسم خورندچنانکه ایشان قوم مرا تعلیم دادند که به بعل قسم خورند، آنگاه ایشان در میان قوم من بنا خواهند شد.۱۶
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
اما اگر نشنوند آنگاه آن امت را بالکل برکنده، هلاک خواهم ساخت.» کلام خداوند این است.۱۷

< Irmiya 12 >