< Irmiya 12 >
1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Tu, ak Kungs, palieci taisns, kad es ar Tevi gribētu tiesāties; tomēr par tiesu ar Tevi gribu runāt. Kāpēc bezdievīgiem ceļš labi izdodas, un visiem, kas dara viltu, labi klājās?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Tu tos esi dēstījis, un tie ir iesakņojušies un aug un nes augļus; Tu gan esi tuvu viņu mutei, bet tālu no viņu sirdīm.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
Bet mani, ak Kungs, Tu pazīsti, mani Tu redzi un pārbaudi manu sirdi, kāda tā ir tavā priekšā. Aizrauj viņus kā avis uz kaušanu un nolieci tos uz nokaušanas dienu!
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Cik ilgi tad zeme lai bēdājās un zāle visur laukā lai savīst? Iedzīvotāju blēdības dēļ lopi un putni iet bojā. Jo tie saka: viņš neredz, kā mums pēcgalā klāsies!
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
Kad tu skrēji ar kājniekiem un tie tevi nokausēja, kā tad tu varētu skrieties ar zirgiem? Un ja tu jūties drošs miera zemē, ko tad tu darīsi Jardānes varenos biezumos?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
Jo, pat tavi brāļi un tavs tēva nams ir neuzticīgi pret tevi un sauc pilnā balsī tev pakaļ. Neuzticies tiem, kad tie laipnīgi ar tevi runā.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
Es Savu namu esmu atstājis un atmetis Savu mantas tiesu un to, ko Mana dvēsele mīļo, nodevis viņa ienaidniekiem rokā.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Mana mantība Man ir palikusi kā lauva mežā; tā savu balsi pret Mani pacēlusi, tādēļ Es to esmu ienīdējis.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Mana mantība Man ir kā raibs putns, kam putni uzkrīt no visām pusēm. Nāciet, sapulcinājaties, visi zvēri laukā, nāciet un ēdiet.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Daudz gani maitājuši Manu vīna dārzu, tie ir saminuši Manu tīrumu, Manu jauko tīrumu tie darījuši par tukšu postažu.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
Tas ir postā, izpostīts tas bēdājās Manā priekšā; visa zeme ir postīta, jo neviena nav, kam sirds to ņem vērā.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Pa visiem tuksneša kalniem postītāji nākuši, jo Tā Kunga zobens rij no viena zemes gala līdz otram, un miera nav nevienai miesai.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
Tie sēj kviešus, bet ērkšķus tie pļauj, tie gan grūti strādā, bet nepelna nekā. Tā tad topat kaunā ar saviem augļiem caur Tā Kunga karsto bardzību.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Tā saka Tas Kungs par visiem maniem nikniem kaimiņiem, kas aizskar to mantību, ko Es esmu devis mantot Saviem Israēla ļaudīm: Es tos izraušu no viņu zemes un Jūda namu Es izraušu no viņu vidus.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
Un notiks, kad Es tos būšu izrāvis, tad Es atkal par tiem apžēlošos, Es tos vedīšu atpakaļ, ikkatru savā daļā un ikkatru savā zemē.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
Un ja tie Manu ļaužu ceļu tikuši(rūpīgi) mācīsies un zvērēs pie Mana Vārda: „Tik tiešām kā Tas Kungs dzīvo!“Tā kā tie Manus ļaudis ir mācījuši pie Baāla zvērēt, - tad tie taps uzņemti Manu ļaužu vidū.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
Bet ja tie neklausīs, tad Es šo tautu izraušu un to pavisam izdeldēšu, saka Tas Kungs.