< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Vous êtes certainement juste, vous, Seigneur, si je dispute avec vous; cependant je vous dirai des choses justes: Pourquoi la voie des impies est-elle prospère, et le bonheur est-il pour tous ceux qui prévariquent, et qui agissent iniquement?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Vous les avez plantés, et ils ont poussé des racines; ils croissent, et font du fruit; vous êtes près de leur bouche, et loin de leurs reins.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
Et vous, Seigneur, vous m’avez connu, vous m’avez vu et vous avez éprouvé que mon cœur est avec vous; assemblez-les comme un troupeau destiné au sacrifice, et consacrez-les pour le jour de la tuerie.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Jusques à quand la terre pleurera-t-elle, et l’herbe de toute la contrée sera-t-elle desséchée, à cause de la méchanceté de ceux qui l’habitent? le quadrupède et le volatile ont été consumés, parce que ces hommes ont dit: Dieu ne verra pas nos derniers moments.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
Si en courant avec les piétons, tu t’es fatigué, comment pourras-tu le disputer de vitesse aux chevaux? mais si dans une terre de paix tu étais en sûreté, que feras-tu au milieu de l’orgueil du Jourdain?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
Car tes frères et la maison de ton père, eux aussi ont combattu contre toi, et ont crié derrière toi à pleine voix; ne les crois pas, lorsqu’ils te donneront de bonnes paroles.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
J’ai laissé ma maison; j’ai abandonné mon héritage; j’ai livré mon âme chérie aux mains de ses ennemis.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Mon héritage est devenu pour moi comme un lion dans la forêt; il a élevé sa voix contre moi; c’est pour cela que je l’ai haï.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Est-ce que mon héritage n’est pas pour moi un oiseau de diverses couleurs? n’est-ce pas un oiseau entièrement coloré? venez, assemblez-vous, vous toutes, bêtes de la terre; hâtez-vous pour dévorer.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Des pasteurs nombreux ont ravagé ma vigne, ils ont foulé aux pieds mon partage; ils ont fait de mon partage précieux un désert solitaire.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
Ils l’ont livré à la dévastation, et il a pleuré sur moi; par la désolation a été désolée toute la terre, parce qu’il n’est personne qui réfléchisse en son cœur.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Sur toutes les voies du désert sont venus des dévastateurs; parce que le glaive du Seigneur dévorera d’une extrémité de la terre à son autre extrémité; il n’y a de paix pour aucune chair.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
Ils ont semé du froment, et ils ont moissonné des épines; ils ont reçu un héritage, et il ne leur servira pas; vous serez confondus par la perte de vos fruits, à cause de la colère de la fureur du Seigneur.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Voici ce que dit le Seigneur contre tous ces voisins très méchants, qui touchent à l’héritage que j’ai distribué à mon peuple d’Israël: Voilà que moi je les arracherai de leur terre, et que j’arracherai la maison de Juda du milieu d’eux.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
Et lorsque je les aurai ainsi déracinés, je me tournerai et j’aurai pitié d’eux, et je les ramènerai l’un dans son héritage, et l’autre dans sa terre.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
Et il arrivera que si, instruits, ils apprennent les voies de mon peuple et jurent par mon nom: Le Seigneur vit! comme ils ont appris à mon peuple à jurer par Baal, ils seront établis au milieu de mon peuple.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
Que s’ils n’écoutent point ma voix, je les extirperai par l’extirpation et par la ruine, dit le Seigneur.

< Irmiya 12 >