< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Seigneur, vous êtes juste; aussi je me défendrai devant vous; je vous demanderai justice. Pourquoi la voie des impies est-elle prospère? pourquoi ceux qui vous ont répudié sont-ils florissants?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Vous les avez plantés, et ils ont pris racine; ils ont engendré, et ils ont produit des fruits. Vous êtes près de leur bouche, et loin de leurs reins.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
Et vous, Seigneur, vous me connaissez, vous avez devant vous éprouvé mon cœur; purifiez-les pour le jour de leur égorgement.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Jusques à quand la terre sera-t-elle en deuil avec des pâturages et des champs desséchés par la malice de ceux qui l'habitent? Les oiseaux et le bétail ont été détruits, parce que les hommes ont dit: Dieu ne verra point. nos voies.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
Tes pieds courent, et te voilà énervé; comment feras-tu donc pour combattre des cavaliers et te confier dans une terre de paix? Que feras-tu contre les débordements du Jourdain?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
Tes frères eux-mêmes et la maison de ton père t'ont méprisé; ils ont eux- mêmes crié contre toi, ils se sont donc unis à ceux qui te poursuivaient par derrière; ne te fie pas à eux, quoiqu'ils te disent de belles paroles.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
J'ai abandonné ma maison; j'ai renoncé à mon héritage; j'ai livré aux mains de ses ennemis celle qui était ma bien-aimée et ma vie.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Mon héritage est devenu contre moi comme le lion dans une forêt; il a rugi contre moi; à cause de cela je l'ai pris en haine.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Mon héritage est-il pour moi un antre d'hyène ou l'enceinte d'une caverne? Allez, rassemblez toutes les bêtes fauves de la terre, et qu'elles viennent dévorer mon héritage.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Maints pasteurs ont ravagé ma vigne; ils ont souillé mon partage; ils ont fait de ma part bien-aimée un désert sans chemin.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
Elle a été livrée au ravage et à la dévastation. Toute la terre a été frappée de ruine à cause de moi, parce que nul homme n'a souci de moi en son cœur.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Ceux qui la dévastaient sont venus par toutes les voies du désert, parce que le glaive du Seigneur va dévorer la terre d'une extrémité à l'autre; il n'est plus de paix pour aucune chair.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
Semez des froments, et vous récolterez des chardons; leur part d'héritage ne leur rapportera rien; soyez confondus à cause de votre orgueil et de vos outrages à la face du Seigneur.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Car ainsi parle le Seigneur contre tous les méchants voisins qui touchent à mon héritage, que j'ai distribué à mon peuple d'Israël: Voilà que je vais les arracher de leur terre, et je rejetterai Juda du milieu d'eux.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
Et voici ce qui arrivera: après les avoir bannis, je changerai, et j'aurai pitié d'eux, et je les ferai rentrer dans leurs demeures, chacun dans son héritage et chacun dans son champ.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
Et ceci arrivera encore: s'ils s'instruisent, s'ils apprennent la voie de mon peuple, et à jurer en mon nom: Vive le Seigneur! comme ils avaient enseigné mon peuple à jurer par le nom de Baal, ils seront édifiés au milieu de mon peuple.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
Et s'il est une de ces nations qui ne se convertisse pas, je la détruirai, et elle sera perdue à jamais.

< Irmiya 12 >