< Irmiya 12 >
1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Forsothe, Lord, thou art iust; if Y dispute with thee, netheles Y schal speke iust thingis to thee. Whi hath the weie of wickid men prosperite? It is wel to alle men that breken the lawe, and doen wickidli?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Thou hast plauntid hem, and thei senten roote; thei encreessen, and maken fruyt; thou art niy to the mouth of hem, and fer fro the reynes of hem.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
And thou, Lord, hast knowe me, thou hast seyn me, and hast preued myn herte with thee. Gadere thou hem togidere as a flok to slayn sacrifice, and halewe thou hem in the dai of sleyng.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Hou long schal the erthe mourne, and ech eerbe of the feeld schal be dried, for the malice of hem that dwellen ther ynne? A beeste is wastid, and a brid, for thei seiden, The Lord schal not se oure laste thingis.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
If thou trauelist rennynge with foot men, hou schalt thou mow stryue with horsis? but whanne thou art sikur in the lond of pees, what schalt thou do in the pride of Jordan?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
For whi bothe thi britheren and the hous of thi fadir, yhe, thei fouyten ayens thee, and crieden with ful vois aftir thee; bileue thou not to hem, whanne thei speken goodis to thee.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
I haue left myn hous, Y haue forsake myn eritage; Y yaf my loued soule in to the hondis of enemyes therof.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Myn eritage is maad as a lioun in the wode to me; it yaf vois ayens me, therfor Y hate it.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Whether myn eritage is a brid of dyuerse colours to me? whether it is a brid died thorou out? Alle beestis of the feeld, come ye, be ye gaderid togidere; haste ye for to deuoure.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Many scheepherdis distrieden my vyner, defouliden my part, yauen my desirable porcioun in to desert of wildirnesse;
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
thei settiden it in to scateryng, and it mourenyde on me; al the lond is desolat bi desolacioun, for noon is that ayenthenkith in herte.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Alle distrieris of the lond camen on alle the weies of desert, for the swerd of the Lord schal deuoure fro the laste part of the lond `til to the laste part therof; no pees is to al fleisch.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
Thei sowiden wheete, and repiden thornes; thei token erytage, and it schal not profite to hem. Ye schulen be schent of youre fruytis, for the wraththe of the stronge veniaunce of the Lord.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
The Lord seith these thingis ayens alle my worst neiyboris, that touchen the eritage which Y departide to my puple Israel, Lo! Y schal drawe hem out of her lond, and Y schal drawe the hous of Juda out of the myddis of hem.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
And whanne Y schal drawe out thilke Jewis, Y schal conuerte, and haue merci on hem; and Y schal lede hem ayen, a man to his eritage, and a man in to his lond.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
And it schal be, if thei `that ben tauyt lernen the weies of my puple, that thei swere in my name, The Lord lyueth, as thei tauyten my puple to swere in Baal, thei schulen be bildid in the myddis of my puple.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
That if thei heren not, Y schal drawe out that folk by drawyng out and perdicioun, seith the Lord.