< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
[are] righteous You O Yahweh if I bring a case to you nevertheless judgments I will speak with you why? [the] way of wicked [people] does it prosper are they at ease? all [those who] act treacherously of treachery.
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
You have planted them also they have taken root they walk also they have produced fruit [are] near you in mouth their and distant from kidneys their.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
And you O Yahweh you know me you see me and you test heart my with you drag away them like sheep to slaughter and set apart them to a day of slaughter.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Until when? will it dry up the land and [the] vegetation of every field will it be dried up from [the] evil of [those who] dwell in it it has dwindled away animals and bird[s] for people have said not he will see end our.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
If with foot soldiers - you have run and they have made weary you and how? will you compete with the horses and in a land of safety you [are] falling to [the] ground and how? will you do in [the] thicket of the Jordan.
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
For also brothers your and [the] house of father your also they they have dealt treacherously with you also they they have called out after you full may not you trust in them for they speak to you good things.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
I have forsaken house my I have abandoned inheritance my I have given [the] beloved one of self my in [the] hand enemies her.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
It has become to me inheritance my like a lion in the forest it has given on me with voice its there-fore I hate it.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
¿ A bird of prey speckled [is] inheritance my to me that [are] bird[s] of prey? all around on it go gather every animal of the field bring [them] for food.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Shepherds many they have ruined vineyard my they have trodden down portion my they have made [the] portion of desire my into a wilderness of desolation.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
He has made it into a desolation it is in mourning on me desolate it has been made desolate all the land for there not [is] anyone [who] puts [it] on heart.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Over all [the] bare heights in the wilderness they have come destroyers for a sword of Yahweh [is] devouring from an end of [the] land and to [the] end of the land not peace [belongs] to any flesh.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
People have sown wheat and thorns they have reaped they have wearied themselves not they have profited and be ashamed from produce your from [the] burning of [the] anger of Yahweh.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Thus - he says Yahweh on all neighbors my evil who touch the inheritance which I gave as an inheritance people my Israel here I [am] about to pluck up them from on land their and [the] house of Judah I will pluck up from among them.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
And it will be after have plucked up I them I will return and I will have compassion on them and I will bring back them everyone to own inheritance his and everyone to own land his.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
And it will be certainly [if] they will learn [the] ways of people my to swear by name my [by] [the] life of Yahweh just as they taught people my to swear by Baal and they will be built in among people my.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
And if not they will listen and I will pluck up the nation that plucking up and destroying [the] utterance of Yahweh.

< Irmiya 12 >