< Irmiya 12 >
1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Thou indeed, O Lord, art just, if I plead with thee, but yet I will speak what is just to thee: Why doth the way of the wicked prosper: why is it well with all them that transgress, and do wickedly?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Thou hast planted them, and they have taken root: they prosper and bring forth fruit: thou art near in their mouth, and far from their reins.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
And thou, O Lord, hast known me, thou hast seen me, and proved my heart with thee: gather them together as sheep for a sacrifice, and prepare them for the day of slaughter.
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
How long shall the land mourn, and the herb of every field wither for the wickedness of them that dwell therein? The beasts and the birds are consumed: because they have said: He shall not see our last end.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
If thou hast wearied with running with footmen, how canst thou contend with horses? and if thou hast been secure in a land of peace, what wilt thou do in the swelling of the Jordan?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
For even thy brethren, and the house of thy father, even they have fought against thee, and have cried after thee with full voice: believe them not when they speak good things to thee.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
I have forsaken my house, I have left my inheritance: I have given my dear soul into the land of her enemies.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
My inheritance is become to me as a lion in the wood: is hath cried out against me, therefore have I hated it.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Is my inheritance to me as a speckled bird? Is it as a bird died throughout? come ye, assemble yourselves, all the beasts of the earth, make haste to devour.
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Many pastors have destroyed my vineyard, they have trodden my portion under foot: they have changed my delightful portion into a desolate wilderness.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
They have laid it waste, and it hath mourned for me. With desolation is all the land made desolate; because there is none that considereth in the heart.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
The spoilers are come upon all the ways of the wilderness, for the sword of the Lord shall devour from one end of the land to the other end thereof: there is no peace for all flesh.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
They have sown wheat, and reaped thorns: they have received an inheritance, and it shall not profit them: you shall be ashamed of your fruits, because of the fierce wrath of the Lord.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Thus saith the Lord against all my wicked neighbors, that touch the inheritance that I have shared out to my people Israel: Behold I will pluck them out of their land, and I will pluck the house of Juda out of the midst of them.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
And when I shall have plucked them out, I will return, and have mercy on them: and I will bring them back, every man to his inheritance, and every man to his land.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
And it shall come to pass, if they will be taught, and will learn the ways of my people, to swear by my name: The Lord liveth, as they have taught my people to swear by baal: that they shall be built up in the midst of my people.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
But if they will not hear, I will utterly pluck out and destroy that nation, saith the Lord.