< Irmiya 12 >

1 Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
Herre! du er retfærdig, naar jeg vil trætte med dig; jeg vil kun tale med dig om Ret: Hvorfor er de ugudeliges Vej lykkelig? hvorfor ere alle de troløse saare trygge?
2 Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
Du plantede dem, de sloge ogsaa Rødder, de gaa frem, de have ogsaa baaret Frugt; du er nær i deres Mund, men langt borte fra deres Indre.
3 Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
Men du, Herre! du kender mig, du ser mig og prøver mit Hjertelag imod dig; bortryk dem som Faar til at slagtes og indvi dem til Drabsdagen!
4 Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
Hvor længe skal Landet sørge og Urterne paa al Marken tørres hen? for deres Ondskabs Skyld, som bo der, ere Dyr og Fugle omkomne; thi de sige: Han ser ikke, hvorledes vor sidste Tid vil blive.
5 “In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
Naar du løb med Fodgængere, og de gjorde dig træt: Hvorledes vil du da kunne kappes med Heste? og i Fredens Land føler du dig vel tryg, men hvorledes vil du gøre det ved Jordans Stolthed?
6 ’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
Thi ogsaa dine Brødre og din Faders Hus, ogsaa disse ere troløse imod dig, ogsaa disse skrige med fuld Røst efter dig; tro dem ikke, naar de tale godt til dig.
7 “Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
Jeg har forladt mit Hus, opgivet min Arv; jeg har givet min Sjæls elskelige i hendes Fjenders Haand.
8 Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
Min Arv er bleven mig som en Løve i Skoven; den har opløftet sin Røst imod mig, derfor hader jeg den.
9 Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
Er min Arv bleven mig som en spraglet Rovfugl? Rovfuglene omringe den; gaar, samler alle vilde Dyr paa Marken, lader dem komme at æde!
10 Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
Mange Hyrder have ødelagt min Vingaard, de have nedtraadt min Ager; de have gjort den Ager; der var min Lyst, til en øde Ørk.
11 Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
Man har gjort den aldeles øde, den sørger over for mig, der den er øde; alt Landet er ødelagt, thi ingen lagde sig det paa Hjerte.
12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
Ødelæggere ere komne over alle nøgne Høje i Ørken; thi Herren har et Sværd, der fortærer fra Jordens ene Ende og indtil Jordens anden Ende; intet Kød har Fred.
13 Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
De saaede Hvede og høstede Torne, de gjorde sig Møje, men det gavner dem ikke, og de skamme sig over deres Indtægt, for Herrens brændende Vredes Skyld.
14 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Saa siger Herren imod alle mine onde Naboer, der antaste den Arv, som jeg har tildelt mit Folk Israel: Se, jeg oprykker dem af deres Land og oprykker Judas Hus af deres Midte.
15 Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
Og det skal ske, efter at jeg har oprykket dem, da vil jeg komme igen og forbarme mig over dem; og jeg vil føre dem tilbage, hver til sin Arv og hver til sit Land.
16 In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
Og det skal ske, dersom de lære mit Folks Veje, saa de Sværge ved mit Navn, „saa sandt som Herren lever”, ligesom de lærte mit Folk at sværge ved Baal: Da skulle de bygges midt iblandt mit Folk.
17 Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.
Men dersom de ikke høre, da vil jeg oprykke et saadant Folk, ja, oprykke og ødelægge det, siger Herren.

< Irmiya 12 >