< Irmiya 11 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Beseda, ki je prišla k Jeremiju od Gospoda, rekoč:
2 “Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
»Poslušaj besede te zaveze in govori možem iz Juda in prebivalcem [prestolnice] Jeruzalem
3 Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
in jim reci: ›Tako govori Gospod, Izraelov Bog: ›Preklet bodi mož, ki ne uboga besed te zaveze,
4 zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
ki sem jo zapovedal vašim očetom na dan, ko sem jih izpeljal iz egiptovske dežele, iz železne talilne peči, rekoč: ›Ubogajte moj glas in jih izvršujte, glede na vse, kar vam zapovedujem. Tako boste moje ljudstvo in jaz bom vaš Bog,
5 Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
da bom lahko izpolnil prisego, ki sem jo prisegel vašim očetom, da jim dam deželo, kjer tečeta mleko in med, kakor je to ta dan.‹« Potem sem odgovoril in rekel: »Tako naj bo, oh Gospod.«
6 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
Potem mi je Gospod rekel: »Razglasi vse te besede po Judovih mestih in ulicah Jeruzalema, rekoč: ›Poslušajte besede te zaveze in jih izpolnjujte.
7 Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
Kajti iskreno sem izpričal vašim očetom na dan, ko sem jih privedel gor iz egiptovske dežele, celó do današnjega dne, [jih] zgodaj vzdigoval in izjavljal, rekoč: ›Ubogajte moj glas.‹
8 Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
Vendar niso ubogali niti nagnili svojega ušesa, temveč so vsi hodili v zamisli svojega zlega srca. Zato bom nanje privedel vse besede te zaveze, ki sem jim jo zapovedal izpolnjevati, toda oni jih niso izpolnjevali.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
Gospod mi je rekel: »Zarota je najdena med Judovimi možmi in med prebivalci Jeruzalema.
10 Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
Obrnili so se nazaj h krivičnostim svojih pradedov, ki so odklanjali poslušati moje besede; in šli za drugimi bogovi, da jim služijo. Izraelova hiša in Judova hiša sta prelomili mojo zavezo, ki sem jo sklenil z njihovimi očeti.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
Zato tako govori Gospod: ›Glej, nanje bom privedel zlo, ki mu ne bodo mogli pobegniti. Čeprav bodo klicali k meni, jim ne bom prisluhnil.
12 Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
Potem bodo Judova mesta in prebivalci Jeruzalema šli in klicali k bogovom, katerim darujejo kadilo. Toda sploh jih ne bodo rešili v času njihove stiske.
13 Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
Kajti glede na število tvojih mest so bili tvoji bogovi, oh Juda; in glede na število ulic [prestolnice] Jeruzalem ste postavili oltarje tisti sramotni stvari, celó oltarje, da zažigate kadilo Báalu.
14 “Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
Zatorej ne moli za to ljudstvo niti ne povzdiguj vpitja ali molitve zanje, kajti jaz jih ne bom poslušal ob času, ko zaradi svoje stiske vpijejo k meni.
15 “Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
Kaj ima moj ljubljeni za početi v moji hiši, ko vidi, da je ona izvrševala nespodobnost s številnimi in je sveto meso odšlo od tebe? Ko počneš zlo, potem se razveseljuješ.
16 Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
Gospod je tvoje ime imenoval: ›Zelena oljka, čeden in lep sad.‹ Z zvokom velikega hrupa je na njej vžgal ogenj in njene mladike so polomljene.
17 Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
Kajti Gospod nad bojevniki, ki te je zasadil, je zoper tebe proglasil zlo, zaradi zla Izraelove hiše in Judove hiše, ki so ga storili zoper sebe, da bi me dražili do jeze v darovanju kadila Báalu.
18 Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
Gospod mi je dal spoznanje o tem in jaz sem to spoznal; takrat si mi kazal njihova dejanja.
19 Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
Toda jaz sem bil podoben jagnjetu ali volu, ki je priveden h klanju in nisem vedel, da so zoper mene snovali naklepe, rekoč: »Uničimo drevo skupaj z njegovim sadom in odsekajmo ga iz dežele živih, da se njegovega imena ne bo več spominjalo.«
20 Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
Toda, oh Gospod nad bojevniki, ki sodiš pravično, ki preizkušaš notranjost in srce, naj vidim tvoje maščevanje na njih, kajti tebi sem razodel svoj primer.
21 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
»Zato tako govori Gospod o možeh iz Anatóta, ki ti strežejo po življenju, rekoč: ›Ne prerokuj v Gospodovem imenu, da ne umreš po naši roki.‹
22 saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
Zato tako govori Gospod nad bojevniki: ›Glej, kaznoval jih bom; mladenič bo umrl pod mečem, njihovi sinovi in njihove hčere bodo umrli od lakote.
23 Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”
Tam ne bo nobenega ostanka izmed njih, kajti nad ljudi iz Anatóta bom privedel zlo, celó leto njihovega obiskanja.‹«

< Irmiya 11 >