< Irmiya 11 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Слово еже бысть от Господа ко Иеремии, глаголющее:
2 “Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
слышите словеса завета сего и глаголите ко мужем Иудиным и ко обитателем Иерусалимским,
3 Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
и речеши к ним: сия глаголет Господь Бог Израилев: проклят муж, иже не послушает словес завета сего,
4 zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
егоже заповедах отцем вашым в день, в оньже изведох их от земли Египетския, от пещи железныя, глаголя: услышите глас Мой и сотворите вся, елика заповедаю вам, и будете Мне в люди, и Аз буду вам в Бога:
5 Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
да утвержду клятву Мою, еюже кляхся отцем вашым, еже дати им землю точащую млеко и мед, якоже есть день сей. И отвещах и рекох: буди, Господи.
6 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
И рече Господь ко мне: прочти вся словеса сия во градех Иудиных и вне Иерусалима, рекий: слышите словеса завета сего и сотворите та:
7 Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
яко свидетелствуя засвидетелствовах отцем вашым в день, в оньже изведох их от земли Египетския, даже до дне сего, заутра востая засвидетелствовах глаголя: слышите глас Мой.
8 Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
И не слышаша, ни приклониша уха своего, но идоша кийждо в стропотстве сердца своего злаго: и наведох на них вся словеса завета сего, егоже заповедах да сотворят, и не сотвориша.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
И рече Господь ко мне: обретено есть совещание (на зло) в мужех Иудиных и во обитающих во Иерусалиме:
10 Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
возвратишася ко беззаконием первым отец своих, иже не хотеша слышати словес Моих, и се, тии поидоша по бозех чуждих, да служат им: и разори дом Израилев и дом Иудин завет Мой, егоже завещах со отцы их.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
Сего ради сия глаголет Господь: се, Аз наведу на них злая, от нихже изыти не возмогут, и возопиют ко Мне, и не услышу их:
12 Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
и пойдут грады Иудины и обитателе Иерусалима и возопиют ко богом, имже тии кадят, иже не спасут их во время скорбей их.
13 Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
По числу бо градов твоих беху бози твои, Иудо, и по числу путий Иерусалимских постависте олтари студныя, олтари на каждение Ваалу.
14 “Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
Ты же не молися о людех сих и не проси о них в мольбе и молитве: не услышу бо во время вопля их ко Мне и во время озлобления их.
15 “Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
Почто возлюбленная в дому Моем сотвори мерзости (многи)? Еда обеты и мяса святая отимут от тебе лукавства твоя, или сими избежиши?
16 Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
Маслину благосенну, красну зраком нарече Господь имя твое, ко гласу обрезания ея: разгореся огнь в ней, велика скорбь на тебе, непотребны быша ветви ея.
17 Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
И Господь Сил, иже насади тебе, глаголал есть на тя зло за злая дому Израилева и дому Иудина, елика сотвориша себе ко прогневанию Мене кадяще Ваалу.
18 Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
Господи, скажи ми, и уразумею: тогда видех начинания их.
19 Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
Аз же, яко агня незлобиво ведомо на заколение, не разумех, яко на мя помыслиша помысл лукавый, глаголюще: приидите и вложим древо во хлеб его и истребим его от земли живущих, и имя его да не помянется ктому.
20 Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
Господь Саваоф, судяй праведно, испытуяй сердца и утробы, да вижду мщение Твое на них, яко к Тебе открых оправдание мое.
21 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
Сего ради сия глаголет Господь на мужы Анафофски ищущыя души моея, глаголющыя: да не пророчествуеши о имени Господни, аще ли же ни, умреши в руках наших.
22 saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
Сего ради сия глаголет Господь Сил: се, Аз посещу на них: юноши их мечем умрут, и сынове их и дщери их скончаются гладом,
23 Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”
и останка не будет от них, наведу бо злая на живущыя во Анафофе в лето посещения их.