< Irmiya 11 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Voici la parole du Seigneur qui est venue à Jérémie, disant:
2 “Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
Écoutez tous les paroles de cette alliance; et toi parle aux hommes de Juda et à ceux qui habitent Jérusalem.
3 Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
Dis-leur: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël: Maudit soit l'homme qui n'écoutera pas les paroles de cette alliance,
4 zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
Que j'ai commandée à vos pères, le jour où je les ai conduits hors de la terre d'Égypte, hors de la fournaise de fer, disant: Soyez dociles à ma voix, et faites toutes les choses que je vous prescris; et vous serez mon peuple, et moi je serai votre Dieu;
5 Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
Afin que j'accomplisse le serment que j'ai fait à vos pères de leur donner une terre où coulent le lait et le miel, comme en ce jour. Et je répondis: Seigneur, qu'il soit ainsi!
6 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
Et le Seigneur me dit: Lis ces paroles dans les villes de Juda. et hors de Jérusalem, disant: Écoutez les paroles de cette alliance, et mettez-les en pratique.
7 Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
Et ils ne les ont point pratiquées.
8 Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
Et ils ne les ont point pratiquées.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
Et le Seigneur me dit: On a découvert un complot tramé contre moi par les hommes de Juda, et ceux qui habitent Jérusalem;
10 Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
Ils sont revenus aux iniquités de leurs pères, qui autrefois n'ont point voulu écouter mes paroles, et voilà qu'ils marchent à la suite des dieux étrangers pour les servir; et la maison d'Israël et la maison de Juda ont déchiré l'alliance que j'avais faite avec leurs pères.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
A cause de cela, ainsi dit le Seigneur: Voilà que je vais amener sur ce peuple des maux dont il ne pourra se tirer; et ils crieront vers moi, et je ne les écouterai pas
12 Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
Et les villes de Juda et les habitants de Jérusalem s'en iront, et ils crieront vers les dieux étrangers, pour qui ils ont brûlé de l'encens; et ces dieux ne les sauveront pas au temps de leurs malheurs.
13 Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
Car, Juda, tu as autant de dieux que de villes; et vous avez dressé autant d'autels pour sacrifier à Baal qu'il y a de rues à Jérusalem.
14 “Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
Et toi, ne prie point pour ce peuple, n'intercède pas pour eux, par oraison ou prière; car je ne les écouterai pas le jour où ils m'invoqueront, le jour de leur affliction.
15 “Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
D'où vient que ma bien-aimée a commis l'abomination dans ma demeure? Les prières ou les chairs sanctifiées effaceront-elles les malices ou te les feront-elles éviter?
16 Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
Le Seigneur t'a donné le nom d'olivier, beau à la vue et donnant un bon ombrage; mais au bruit de son ébranchement, un feu a été allumé contre lui; grande est ton affliction, car ses rameaux sont devenus inutiles.
17 Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
Et le Seigneur, qui t'avait plantée, a prononcé des maux contre toi en punition de ta méchanceté, maison d'Israël, et de la tienne, maison de Juda; car ils se sont nui à eux-mêmes pour m'irriter, en brûlant de l'encens à Baal.
18 Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
Seigneur, instruisez-moi, et je saurai. Et alors j'ai vu leurs machinations contre moi.
19 Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
Mais moi, comme un agneau innocent conduit au sacrifice, je ne remarquais rien. Ils avaient conçu contre moi un mauvais dessein, disant: Allons, mêlons du bois à son pain, effaçons-le de la terre des vivants, et que nul ne se souvienne de son nom.
20 Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
Seigneur, qui jugez selon la justice, qui sondez les reins et les cœurs, puissé-je voir la vengeance que vous tirerez d'eux; car je vous ai exposé ma cause.
21 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
A cause de cela, voici ce que dit le Seigneur contre les hommes d'Anathoth qui en veulent à ma vie, et qui disent: Tu cesseras de prophétiser au nom du Seigneur, sinon tu périras de nos mains.
22 saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
Et moi, voilà que je les visiterai; leurs jeunes gens mourront par le glaive, et leurs fils et leurs filles mourront de faim.
23 Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”
Et il ne restera rien d'eux, parce que je vais amener des maux sur les habitants d'Anathoth, en l'année où je les visiterai.

< Irmiya 11 >