< Irmiya 11 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
La parole qui fut adressée à Jérémie de la part de Yahweh, en ces termes:
2 “Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
Entendez les paroles de cette alliance, et parlez aux hommes de Juda et aux habitants de Jérusalem.
3 Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
Et tu leur diras: Ainsi parle Yahweh, Dieu d’Israël: Maudit soit l’homme qui n’écoute pas les paroles de cette alliance,
4 zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
que j’ai prescrites à vos pères, au jour où je les ai fait sortir de la terre d’Égypte, de la fournaise à fer, en leur disant: Écoutez ma voix et faites ces choses, selon tout ce que je vous commanderai, et vous serez mon peuple, et moi je serai votre Dieu,
5 Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
afin que j’accomplisse le serment que j’ai fait à vos pères de leur donner un pays où coulent le lait et le miel, comme cela se voit aujourd’hui. Et je répondis: « Oui! Yahweh! »
6 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
Et Yahweh me dit: Crie toutes ces paroles dans les villes de Juda et dans les rues de Jérusalem, en disant: Écoutez les paroles de cette alliance et mettez-les en pratique.
7 Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
Car j’ai instamment averti vos pères depuis le jour où je les ai fait monter du pays d’Égypte jusqu’à ce jour; je les ai sans cesse avertis, en disant: Écoutez ma voix.
8 Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
Et ils n’ont ni écouté ni prêté l’oreille; chacun d’eux a marché selon l’opiniâtreté de son mauvais cœur. Et j’ai exécuté sur eux toutes les paroles de cette alliance, que je leur avait prescrit d’observer, et qu’ils n’ont pas observée.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
Yahweh me dit: Il s’est trouvé une conjuration chez les hommes de Juda, et chez les habitants de Jérusalem.
10 Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
Ils sont retournés aux iniquités de leurs premiers pères qui ont refusé d’écouter mes paroles, et ils sont allés après d’autres dieux pour les servir. La maison d’Israël et la maison de Juda ont violé mon alliance que j’avais conclue avec leurs pères.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
C’est pourquoi ainsi parle Yahweh: Voici que je vais amener sur eux des malheurs, dont ils ne pourront sortir; et, s’ils crient vers moi, je ne les écouterai pas.
12 Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
Et les villes de Juda et les habitants de Jérusalem iront invoquer les dieux auxquels ils offrent de l’encens; mais ces dieux ne les sauveront sûrement pas, au temps de leur malheur.
13 Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
Car aussi nombreux que tes villes, sont tes dieux, ô Juda, et aussi nombreux que les rues de Jérusalem, sont les autels que vous avez dressés à une infâme idole, les autels que vous avez dressés pour encenser Baal.
14 “Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
Et toi, n’intercède pas pour ce peuple, et n’élève point en leur faveur de supplication ni de prière; car je n’écouterai point lorsqu’ils m’invoqueront, au temps de leur malheur.
15 “Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
Qu’est-ce que ma bien-aimée a à faire dans ma maison? Des fourberies? Est-ce que les vœux et la chair sacrée enlèveront de dessus toi tes malheurs, que tu puisses te livrer à l’allégresse?
16 Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
Olivier verdoyant, orné de beaux fruits: c’est le nom que t’avait donné Yahweh. Au bruit d’un grand fracas, il y met le feu, et ses rameaux sont brisés.
17 Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
Yahweh des armées, qui t’avait planté, a décrété le malheur contre toi, à cause du crime de la maison d’Israël et de la maison de Juda, qu’ils ont commis pour m’irriter, en encensant Baal.
18 Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
Yahweh m’en a informé, et je l’ai su; … alors vous m’avez fait connaître leurs œuvres!
19 Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
Moi, j’étais comme un agneau familier, qu’on mène à la boucherie, et je ne savais qu’ils formaient des desseins contre moi: « Détruisons l’arbre avec son fruit! Retranchons-le de la terre des vivants, et qu’on ne se souvienne plus de son nom! »
20 Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
Mais Yahweh des armées juge avec justice; il sonde les reins et les cœurs; je verrai la vengeance que vous tirerez d’eux, car c’est à vous que j’ai confié ma cause.
21 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
C’est pourquoi ainsi parle Yahweh au sujet des hommes d’Anathoth qui en veulent à ta vie et qui disent: « Ne prophétise pas au nom de Yahweh, si tu ne veux mourir de notre main! »
22 saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
C’est pourquoi ainsi parle Yahweh des armées: Je vais les punir; les jeunes hommes mourront par l’épée; leurs fils et leurs filles mourront de faim.
23 Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”
Aucun d’eux n’échappera; car j’amènerai le malheur sur les hommes d’Anathoth, l’année où je les visiterai.

< Irmiya 11 >