< Irmiya 11 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Det Ord, som kom til Jeremias fra Herren, saa lydende:
2 “Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
Hører denne Pagts Ord, og taler til Judas Mænd og til Jerusalems Indbyggere!
3 Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
Og du skal sige til dem: Saa siger Herren, Israels Gud: Forbandet være den Mand, som ikke adlyder denne Pagts Ord,
4 zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
hvilken jeg bød eders Fædre paa den Dag, da jeg udførte dem af Ægyptens Land, fra Jernovnen, sigende: Adlyder min Røst, og gører disse Ting efter alt det, som jeg byder eder, saa skulle I være mit Folk, og jeg vil være eders Gud,
5 Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
paa det jeg kan stadfæste den Ed, som jeg svor eders Fædre, at jeg vilde give dem et Land, som flyder med Mælk og Honning, som det ses paa denne Dag; og jeg svarede og sagde: Amen, Herre!
6 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
Og Herren sagde til mig: Udraab alle disse Ord i Judas Stæder og paa Gaderne i Jerusalem, og sig: Hører denne Pagts Ord, og gører derefter!
7 Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
Thi jeg vidnede højt for eders Fædre paa den Dag, jeg førte dem op af Ægyptens Land, indtil denne Dag, tidligt og ideligt, sigende: Adlyder min Røst!
8 Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
Men de adløde ikke og bøjede ikke heller deres Øre, men hver vandrede i sit onde Hjertes Stivhed; og over dem lod jeg komme alle denne Pagts Ord, som jeg havde befalet at gøre efter, men som de ikke gjorde.
9 Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
Og Herren sagde til mig: Der findes en Sammensværgelse iblandt Judas Mænd og iblandt Jerusalems Indbyggere.
10 Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
De have vendt om til at begaa Misgerninger som deres Forfædre, der vægrede sig ved at adlyde mine Ord, og de have vandret efter andre Guder for at tjene dem; Israels Hus og Judas Hus have brudt min Pagt, som jeg gjorde med deres Fædre.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
Derfor siger Herren saaledes: Jeg lader en Ulykke komme paa dem, fra hvilken de ikke skulle kunne undkomme; og de skulle raabe til mig, og jeg skal ikke bønhøre dem.
12 Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
Og Judas Stæder og Indbyggerne i Jerusalem skulle gaa og raabe til de Guder, for hvilke de gjorde Røgelse; men de skulle ikke frelse dem i deres Ulykkes Tid.
13 Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
Thi saa mange som dine Stæder ere, saa mange ere dine Guder, Juda! og saa mange Gader, som der er i Jerusalem, saa mange Altre have I opsat til Skændsel, Altre til at gøre Røgelse for Baal.
14 “Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
Og du maa ikke bede for dette Folk og ikke opløfte Skrig eller Bøn for dem; thi jeg vil ikke høre paa den Tid, naar de raabe paa mig over deres Ulykke.
15 “Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
Hvad er der for min elskelige i mit Hus? At de store øve det, som er Skændighed og lade det hellige Kød gaa bort fra dig; thi naar dit Onde kommer, da fryde du dig!
16 Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
Herren kaldte dit Navn et grønt Olietræ, smukt ved dejlig Frugt; med stort Bulders Lyd har han antændt en Ild om det, og de have sønderbrudt dets Grene.
17 Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
Og den Herre Zebaoth, som plantede dig, har talt ondt over dig, for Israels Hus's og Judas Hus's Ondskabs Skyld, som de bedreve for at opirre mig, idet de gjorde Røgelse for Baal.
18 Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
Og Herren lod mig det vide, saa jeg ved det; dengang lod du mig se deres Idrætter.
19 Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
Og jeg var som et tamt Lam, der føres hen at slagtes, og jeg vidste ikke, at de havde optænkt Anslag imod mig og sagt: Lader os ødelægge Træet med dets Frugt og udrydde ham af de levendes Land, at hans Navn ikke ydermere ihukommes.
20 Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
Men, Herre Zebaoth, du retfærdige Dommer, som prøver Nyrer og Hjerte! jeg skal se din Hævn paa dem: Thi dig har jeg forelagt min Sag.
21 “Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
Derfor siger Herren saaledes om de Mænd i Anathoth, som søge efter dit Liv og sige: Spaa ikke i Herrens Navn, saa skal du ikke dø ved vor Haand;
22 saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
ja, derfor siger den Herre Zebaoth saaledes: Se, jeg vil hjemsøge dem; deres unge Karle skulle dø ved Sværdet, deres Sønner og deres Døtre skulle dø ved Hunger;
23 Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”
og intet skal blive tilovers af dem; thi jeg vil lade Ulykke komme over de Mænd i Anathoth i deres Hjemsøgelses Aar.