< Irmiya 10 >

1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Ouvi a palavra que o Senhor vos falla a vós, ó casa d'Israel.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
Assim diz o Senhor: Não aprendaes o caminho das nações, nem vos espanteis dos signaes dos céus: porque com elles se atemorisam as nações.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
Porque os estatutos dos povos são vaidade: pois corta-se do bosque um madeiro, obra das mãos do artifice, com machado;
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
Com prata e com oiro o enfeitam, com pregos e com martelos o firmam, para que não se abale.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
São como a palma da obra magica, porém não podem fallar; necessitam de ser levados aos hombros, porquanto não podem andar; não tenhaes temor d'elles, pois não podem fazer mal, nem tão pouco teem poder de fazer bem.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Pois ninguem ha similhante a ti, ó Senhor: tu és grande, e grande o teu nome em força.
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Quem te não temeria a ti, ó Rei das nações? pois isto te compete a ti; porquanto entre todos os sabios das nações, e em todo o seu reino, não ha similhante a ti.
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Pois juntamente todos se embruteceram e vieram a enlouquecer: ensino de vaidades é o madeiro.
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
Trazem prata estendida de Tarsis e oiro d'Uphaz, para obra do artifice, e das mãos do fundidor: fazem seus vestidos d'azul celeste e purpura; obra de sabios são todos elles.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
Porém o Senhor Deus é a verdade; elle mesmo é o Deus vivo e o Rei eterno; do seu furor treme a terra, e as nações não podem supportar a sua indignação.
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
Assim lhes direis: Os deuses que não fizeram os céus e a terra perecerão da terra e de debaixo d'este céu.
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
Elle é aquelle que fez a terra com o seu poder, que estabeleceu o mundo com a sua sabedoria, e com a sua intelligencia estendeu os céus.
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
Dando elle a sua voz, logo ha arroido de aguas no céu, e faz subir os vapores da extremidade da terra: faz os relampagos juntamente com a chuva, e faz sair o vento dos seus thesouros.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Todo o homem se embruteceu, e não tem sciencia; envergonha-se todo o fundidor da imagem d'esculptura; porque sua imagem fundida mentira é, e não ha espirito n'ellas.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Vaidade são, obra d'enganos: no tempo da sua visitação virão o perecer.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Não é similhante a estes a porção de Jacob; porque elle é o que o formou, e Israel é a vara da sua herança: Senhor dos Exercitos é o seu nome.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
Ajunta da terra a tua mercadoria, ó moradora na fortaleza.
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
Porque assim diz o Senhor: Eis que d'esta vez lançarei como com funda aos moradores da terra, e os angustiarei, para que venham a achal-o, dizendo:
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
Ai de mim por causa do meu quebrantamento! a minha chaga me causa grande dôr; e eu havia dito: Certamente enfermidade é esta que poderei supportar.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Já a minha tenda está destruida, e todas as minhas cordas se romperam; já os meus filhos sairam de mim, e não são; ninguem ha mais que estenda a minha tenda, nem que levante as minhas cortinas.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Porque os pastores se embruteceram, e não buscaram ao Senhor: por isso não prosperaram, e todos os seus gados se espalharam.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Eis que vem uma voz de fama, grande tremor da terra do norte, para fazer das cidades de Judah uma assolação, uma morada de dragões.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Bem sei eu, ó Senhor, que não é do homem o seu caminho nem do homem que caminha o dirigir os seus passos.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Castiga-me, ó Senhor, porém com medida, não na tua ira, para que me não reduzas a nada.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Derrama a tua indignação sobre as nações que te não conhecem, e sobre as gerações que não invocam o teu nome; porque comeram a Jacob, e o devoraram, e o consumiram, e assolaram a sua morada.

< Irmiya 10 >