< Irmiya 10 >

1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Ecoutez la parole que le Seigneur a dite sur vous, maison d’Israël.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
Voici ce que dit le Seigneur: N’apprenez pas les voies des nations, et ne redoutez pas les signes du ciel, que craignent les nations;
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
Parce que les lois des peuples sont vaines; parce que l’œuvre de la main d’un ouvrier habile a coupé du bois de la forêt avec la hache.
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
Elle l’a orné d’or et d’argent; elle en a joint les parties avec des clous et des marteaux, afin qu’il ne se désunisse pas.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
Ces œuvres ont été fabriquées en forme de palmier; elles ne parleront pas; on les portera, on les enlèvera, parce qu’elles ne peuvent marcher; ne les craignez donc pas, parce qu’elles ne peuvent faire ni mal ni bien.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Il n’est pas de semblable à vous, Seigneur; vous êtes grand, vous, et grand est votre nom en puissance.
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Qui ne vous craindra pas, ô roi des nations? car à vous est la gloire parmi tous les sages des nations, et dans tous leurs royaumes nul n’est semblable à vous.
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Tous également seront reconnus insensés et stupides; c’est une doctrine vaine que leur bois.
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
On apporte de l’argent enveloppé de Tharsis et de l’or d’Ophaz, ouvrage d’un artisan, et de la main d’un ouvrier en airain; l’hyacinthe et la pourpre sont leur vêtement; tout cela est un ouvrage d’artisans.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
Mais le Seigneur est le vrai Dieu; lui-même est le Dieu vivant et le roi éternel; par son indignation la terre sera ébranlée, et les nations ne soutiendront pas sa menace.
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
Ainsi donc tu leur diras: Que les dieux qui n’ont pas fait les deux et la terre disparaissent de la terre et de ce qui est sous le ciel.
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
C’est le Seigneur qui fait la terre dans sa puissance, qui prépare le globe dans sa sagesse, et étend les cieux par sa prudence.
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
À sa voix il met une quantité d’eaux dans le ciel, et il élève les nuées des extrémités de la terre; les éclairs, il les résout en pluie, et il fait sortir les vents de ses trésors.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Tout homme est devenu insensé par sa propre science; tout artisan a été confondu par son image taillée au ciseau, parce que c’est une chose fausse qu’il a fondue, et la vie n’y est pas.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Ce sont des choses vaines, un ouvrage digne de risée; au temps de sa visite elles périront.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Il n’est pas semblable à ces choses, celui qui est la part de Jacob; car celui qui a formé toutes choses, c’est lui-même, et Israël est la verge de son héritage; et le Seigneur des armées est son nom.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
Rassemble de la terre ta confusion, toi qui restes assiégée;
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
Parce que voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je jetterai au loin les habitants de cette terre cette fois; et je les affligerai, de telle sorte qu’on les saisira.
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
Malheur à moi, à cause de ma ruine; ma plaie est très grave. Mais moi j’ai dit: Ce mal vient entièrement de moi, et je le supporterai.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Mon tabernacle a été dévasté, mes cordages ont été rompus; mes fils sont sortis de mon enceinte, et n’existent pas; il n’y a personne qui tende désormais ma tente et dresse mes pavillons.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Parce que les pasteurs ont agi en insensés, et qu’ils n’ont pas cherché le Seigneur; à cause de cela ils ont été sans intelligence, et tout leur troupeau a été dispersé.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Voici qu’une voix retentissante vient, ainsi qu’un grand tumulte, de la terre de l’aquilon, pour faire des cités de Juda une solitude, et une demeure de dragons.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Je sais, Seigneur, qu’à l’homme n’appartient pas sa voie, et qu’il n’est pas de l’homme de marcher et de diriger ses pas.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Châtiez-moi, Seigneur, mais cependant dans votre justice, et non dans votre fureur, de peur que vous ne me réduisiez au néant.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Répandez votre indignation sur les nations qui ne vous ont pas connu, et sur les provinces qui n’ont pas invoqué votre nom; parce qu’elles ont mangé Jacob, et l’ont dévoré, et l’ont consumé, et ont dissipé sa gloire.

< Irmiya 10 >