< Irmiya 10 >

1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Maison d'Israël, écoutez la parole que l'Eternel a prononcée sur vous.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
Ainsi a dit l'Eternel: n'apprenez point les façons de faire des nations, et ne soyez point épouvantés des signes des cieux, sous ombre que les nations en sont épouvantées.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
Car les statuts des peuples [ne] sont [que] vanité, parce qu'on coupe du bois de la forêt pour le mettre en œuvre avec la hache;
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
Puis on l'embellit avec de l'argent et de l'or, et on le fait tenir avec des clous et à coups de marteau, afin qu'il ne remue point.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
Ils sont façonnés tout droits comme un palmier, et ils ne parlent point; on les porte par nécessité, à cause qu'ils ne peuvent pas marcher; ne les craignez point, car ils ne font point de mal, et aussi il n'est pas en leur pouvoir de faire du bien.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Il n'y a point de [dieu] semblable à toi, ô Eternel! tu es grand, et ton Nom est grand en force.
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Qui ne te craindrait, Roi des nations, car cela t'est dû? parce qu'entre tous les plus sages des nations, et dans tous leurs Royaumes il n'y en a point de semblable à toi.
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Et ils sont tous ensemble abrutis, et devenus fous; le bois [ne leur] apprend que des vanités.
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
L'argent qui est étendu en plaques, est apporté de Tarsis, et l'or est apporté d'Uphaz, pour être mis en œuvre par l'ouvrier, et par les mains du fondeur; et la pourpre et l'écarlate est leur vêtement; toutes ces choses sont l'ouvrage de gens adroits.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
Mais l'Eternel est le Dieu de vérité, [c'est] le Dieu vivant, et le Roi éternel; la terre sera ébranlée par sa colère, et les nations ne pourront soutenir son indignation.
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
Vous leur direz ainsi: les dieux qui n'ont point fait les cieux et la terre périront de la terre, et de dessous les cieux.
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
[Mais l'Eternel] est celui qui a fait la terre par sa vertu, qui a formé le monde habitable par sa sagesse, et qui a étendu les cieux par son intelligence;
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
Sitôt qu'il a fait éclater sa voix [il y a] un grand bruit d'eaux dans les cieux; après qu'il a fait monter du bout de la terre les vapeurs, il fait briller l'éclair avant la pluie, et il tire le vent hors de ses trésors.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Tout homme se montre abruti dans sa science; tout fondeur est rendu honteux par les images taillées; car ce qu'ils font est une fausseté, et il n'y a point de respiration en elles.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Elles ne sont que vanité, et un ouvrage propre à abuser; elles périront au temps de leur visitation.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
La portion de Jacob n'est point comme ces choses-là; car c'est celui qui a tout formé, et Israël est le lot de son héritage; son nom est l'Eternel des armées.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
Toi qui habites en un lieu fort, retire du pays ta marchandise.
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
Car ainsi a dit l'Eternel: voici, je m'en vais à cette fois jeter [au loin, comme] avec une fronde, les habitants du pays, et je les mettrai à l'étroit, tellement qu'ils le trouveront.
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
Malheur à moi, [diront-ils], à cause de ma plaie, ma plaie est douloureuse. Mais moi j'ai dit: quoi qu'il en soit, c'est une maladie qu'il faut que je souffre.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Ma tente est gâtée; tous mes cordages sont rompus; mes enfants sont sortis d'auprès de moi, et ne sont plus; il n'y a plus personne qui dresse ma tente, et qui élève mes pavillons.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Car les pasteurs sont abrutis, et n'ont point recherché l'Eternel; c'est pourquoi ils ne se sont point conduits sagement, et tous leurs pâturages ont été dissipés.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Voici, un bruit de certaines nouvelles est venu, avec une grande émotion de devers le pays d'Aquilon, pour ravager les villes de Juda, et en faire une retraite de dragons.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Eternel, je connais que la voie de l'homme ne dépend pas de lui, et qu'il n'est pas au pouvoir de l'homme qui marche, de diriger ses pas.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Ô Eternel! châtie-moi, mais [que ce soit] par mesure, [et] non en ta colère, de peur que tu ne me réduises à rien.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Répands ta fureur sur les nations qui ne te connaissent point, et sur les familles qui n'invoquent point ton Nom; car ils ont dévoré Jacob, ils l'ont, dis-je, dévoré et consumé, et ils ont mis en désolation son agréable demeure.

< Irmiya 10 >