< Irmiya 10 >
1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Écoutez la parole du Seigneur, celle qu'il a dite pour vous, maison d'Israël.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
Voici ce que dit le Seigneur: Ne vous instruisez point selon les voies des gentils; ne craignez point les signes du ciel qu'ils adorent en se prosternant.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
Car les objets du culte des gentils sont choses vaines: c'est un arbre abattu dans la forêt, œuvre d'un charpentier;
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
C'est un métal fondu, orné d'argent ou d'or battus; et on les a affermis avec des marteaux et des clous, et ils ne bougeront plus.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
C'est de l'argent travaillé, il ne marchera jamais; c'est une image en argent de Tharsis; viendra aussi l'or de Mophaz, et la main du fondeur; ce sont œuvres d'artistes, revêtues d'hyacinthe et de pourpre. Elles ne peuvent aller qu'on ne les porte. Ne les craignez point, elles ne vous feront point de mal, et il n'y a pas de bien à en attendre.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
Dites-leur: Que des dieux qui n'ont créé ni le ciel ni la terre périssent sur la terre et sous le ciel
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
C'est le Seigneur qui a fait la terre par sa puissance, qui a affermi le monde par sa sagesse, qui a étendu le ciel par son intelligence,
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
Et l'amas des eaux sous le ciel. Et il a rassemblé les nuages des extrémités de la terre; il a mêlé les éclairs à la pluie, et tiré la lumière de ses trésors.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Tout homme n'est qu'un insensé en fait de science; l'orfèvre a été confondu dans ses idoles; car il a fait des choses mensongères, des corps sans vie.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Vaines et ridicules sont ces œuvres, et au jour de la visite elles périront.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Tel n'est point le partage de Jacob, parce que le Créateur de toutes choses est lui-même son héritage; son nom est le Seigneur.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
Il a recueilli du dehors ta substance qui était en des vases choisis.
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
Or ainsi parle le Seigneur: Voilà que je vais accabler de tribulations les habitants de cette terre, afin que ta plaie soit mise à nu.
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
Malheur sur ta meurtrissure, ta plaie est douloureuse. Et moi j'ai dit: En vérité c'est ta blessure, c'est elle qui te punit.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Ton tabernacle est dévasté, il a péri, et toutes les tentures en sont déchirées. Mes fils et mes brebis ne sont plus, il n'y a plus de place pour mon tabernacle ni pour ses tentures.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Parce que mes pasteurs ont été insensés et n'ont point cherché le Seigneur, à cause de cela le troupeau a été sans intelligence et les agneaux dispersés.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Voilà qu'un bruit de voix arrive; et la terre a tremblé du côté de l'aquilon, pour rendre désertes les villes de Juda, et en faire la demeure des autruches.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Seigneur, je sais que la voie de l'homme n'est point en lui, et que ce n'est point un homme qui viendra pour redresser sa marche.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Châtiez-nous, Seigneur, mais avec justice, et non avec colère, afin que nous ne soyons pas réduits à un petit nombre.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Versez votre courroux sur les nations qui ne vous connaissent pas, et sur les races qui n'ont point invoqué votre nom; car celles-ci ont dévoré Jacob, elles l'ont épuisé, et de son pâturage elles ont, fait une solitude.