< Irmiya 10 >

1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
You people of Israel, listen to what Yahweh says:
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
“Do not act like the people of [other] nations act, and do not be terrified by strange/unusual things that you see in the sky, even though they cause the [people of other] nations to be terrified.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
The customs of the people [of other nations] are worthless. [For example], they cut down a tree in the forest. Then a [skilled] worker/craftsman [cuts a section of it and] uses his chisel to carve an idol from that section.
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
[Then] people decorate the idol with silver and gold. [Then] they fasten it securely with nails in order that it will not topple/fall over.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
[Then] the idol [stands there] like [SIM] a scarecrow in a field of cucumbers/melons! It cannot speak, and people must carry it, because it cannot walk. Do not be afraid of idols, because they cannot harm [anyone], and they cannot do [anything] good [to help anyone].”
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Yahweh, there is no one like you. You [MTY] are great, and you are very powerful.
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
You are the king of all the nations! Everyone should [RHQ] revere you, because that is what you deserve. Among all the wise people on the earth and in all the kingdoms where they live, (there is no one like you./who can compare with you?)
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
Those people who [think that they are] very wise [IRO] are stupid and foolish [DOU]. The idols that they worship are only made of wood! Those idols certainly cannot teach them anything.
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
People hammer into thin sheets silver from Tarshish and gold from Uphaz, and then they give those sheets of silver and gold to skilled workers/craftsmen to cover the idols. Then they put on those idols expensive purple robes that are made by skilled workers.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
But Yahweh is the [only] true God; he is the all-powerful God, the king [who rules] forever. When he is angry, [all] the earth shakes/quakes; and [the people of] the nations cannot endure [what he does] when he is angry [with them].
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
[You Israeli people], tell this to those people: “Those idols did not make the sky and the earth, and they will disappear from the earth.”
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
But [Yahweh] made the earth by his power; he established it [firmly] by his wisdom and stretched out the sky by his understanding.
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
When he speaks [loudly], there is thunder in the sky; he causes clouds to form over every part of the earth. He sends lightning with the rain and releases the winds from his storehouses.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
People are senseless and know very little [HYP]; those who make idols are always disappointed because their idols do nothing for them. The images/statues that they make are not real [gods]; they are lifeless.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Idols are worthless; they deserve to be ridiculed; there will be a time when they [all] will be destroyed.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
But the God whom we Israelis worship is not like those idols; he is the one who created everything [that exists]; we, the tribe/people of Israel, belong to him; he is the Commander of the armies of angels.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
[Yahweh says this to the people of Jerusalem]: “The army of your enemies surrounds your city, so gather up your possessions [and prepare] to leave the city.
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
I will soon throw you out of this land and cause you to experience great troubles, with the result that you will have severe pain (OR, none of you will be left here).”
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
[The people replied, “It is as though] we have been [badly] wounded, and we are very grieved; [It is as though] we have a very serious illness, and we must endure the pain.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
[It is as though] our [great] tent is destroyed; the ropes [that held it up] have been cut; our children have gone away from us and will not return; there are no people left to rebuild our great tent.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Our leaders [MET] no [longer] have any sense; they no [longer] ask Yahweh [to (guide them/tell them what to do)], so they will no [longer] prosper, and all those over whom they rule [MET] will be scattered.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Listen! [Our enemies’ armies] in the north are making a [very] big noise/commotion [as they march toward us]. The towns in Judah will be destroyed, [and they will become] a place where jackals/wolves live.”
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Yahweh, I know that no person controls what will happen to him; no one is able to direct the events that he will experience.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
[So] correct/discipline us, but do it gently. Do not correct/punish us when you are angry, because we would die if you did that.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Punish [MTY] [all] the nations whose people do not acknowledge/say that you are God; punish all the nations whose people do not worship you, because they are completely destroying [DOU] [us people of] Israel and they are causing our land to soon be only a desert.

< Irmiya 10 >