< Irmiya 1 >

1 Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
Ord av Jeremias, Hilkias' sønn, en av prestene i Anatot i Benjamins land.
2 Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
Herrens ord kom til ham i de dager da Josias, Amons sønn, var konge i Juda, i det trettende år av hans regjering,
3 da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
og siden i de dager da Jojakim, Josias' sønn, var konge i Juda, inntil enden av Judas konge Sedekias', Josias' sønns ellevte år, da Jerusalems innbyggere blev bortført i den femte måned.
4 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Herrens ord kom til mig, og det lød så:
5 “Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
Før jeg dannet dig i mors liv, kjente jeg dig, og før du kom ut av mors skjød, helliget jeg dig; jeg satte dig til en profet for folkene.
6 Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
Men jeg sa: Akk, Herre, Herre! Se, jeg forstår ikke å tale; for jeg er ung.
7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
Da sa Herren til mig: Si ikke: Jeg er ung! Men til alle dem jeg sender dig til, skal du gå, og alt det jeg byder dig, skal du tale.
8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
Frykt ikke for dem, for jeg er med dig og vil redde dig, sier Herren.
9 Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
Og Herren rakte ut sin hånd og rørte ved min munn, og Herren sa til mig: Se, jeg legger mine ord i din munn.
10 Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
Se, jeg setter dig idag over folkene og over rikene til å rykke op og rive ned, til å ødelegge og bryte ned, til å bygge og til å plante.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så: Hvad ser du, Jeremias? Jeg svarte: Jeg ser en stav av det våkne tre.
12 Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
Da sa Herren til mig: Du har sett rett; for jeg vil våke over mitt ord, så jeg fullbyrder det.
13 Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
Og Herrens ord kom til mig annen gang: Hvad ser du? Jeg svarte: Jeg ser en kokende gryte, og den er vendt hit fra nord.
14 Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
Og Herren sa til mig: Fra nord skal ulykken slippes løs over alle landets innbyggere.
15 Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
For se, jeg kaller på alle folkestammer i rikene mot nord, sier Herren, og de skal komme og sette hver sin stol ved inngangen til Jerusalems porter og mot alle dets murer rundt omkring og mot alle Judas byer.
16 Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
Og jeg vil avsi mine dommer over dem for all deres ondskaps skyld, fordi de forlot mig og brente røkelse for andre guder og tilbad sine henders verk.
17 “Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
Men du skal omgjorde dine lender og stå op og tale til dem alt det jeg byder dig; vær ikke redd for dem, så jeg ikke skal gjøre dig redd for dem!
18 Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
Og se, jeg gjør dig idag til en fast borg og til en jernstøtte og til en kobbermur mot det hele land, mot Judas konger, mot dets høvdinger, mot dets prester og mot folket i landet.
19 Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
Og de skal stride mot dig, men ikke få overhånd over dig; for jeg er med dig, sier Herren, og vil redde dig.

< Irmiya 1 >